Yayin da aka nemi ta yi tsokaci game da karuwar zaman tankiya a tsakanin Amurka da Iran a yau Alhamis, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin na sa ido sosai kan abubuwan da ke faruwa a Iran, kuma kasar na adawa da amfani ko barazanar amfani da karfin tuwo a huldar kasa da kasa.
A yayin taron manema labarai na yau da kullum, Mao ta ce, a ko da yaushe kasar Sin tana ba da shawarar warware matsaloli ta hanyar siyasa da diflomasiyya.
Ta kara da cewa, al’ummomin kasashen Sin da Iran na da dadaddiyar abota ta gargajiya. Kasar Sin tana goyon bayan gwamnati da al’ummar Iran wajen kiyaye zaman lafiyar kasarsu da hakkoki da kuma muradunsu. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














Discussion about this post