Wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD Fu Cong ya bayyana cewa, kusan shekaru uku ke nan bayan barkewar ricikin Sudan, lamarin da ya haifar da masifa mai tsanani ga jama’ar kasar. Don haka, kasar Sin ta ba da shawarar cewa, kamata ya yi kasashen duniya su tsaya kan ra’ayoyin bai daya guda biyar don neman hanyar da ta dace ta warware rikicin na dogon lokaci.
Fu Cong ya fadi haka ne a lokacin da kwamitin sulhu ke dudduba batun kasar Sudan a jiya Alhamis, inda ya kara yin bayani kan ra’ayoyi biyar cewa, da farko, a tsaya kan ra’ayin tsagaita bude wuta da dakatar da yaki ba tare da bata lokaci ba. Na biyu, a tsaya kan ra’ayin sassauta tabarbarewar yanayin jin kai. Na uku, a tsaya kan ra’ayin karfafa sulhuntawa. Na hudu, a tsaya kan ra’ayin a bar jama’ar Sudan su jagoranci yunkurin warware rikicin. Na biyar, a tsaya kan ra’ayin yin la’akari da ci gaba da kuma tsaro baki daya.
Fu Cong ya kara da cewa, yanzu dai musulmai na wurare daban daban na duniya, ciki har da Sudan sun shiga watan Ramadan. Don haka, kasar Sin ta kara yin kira ga bangarori daban daban masu ruwa da tsaki su tsagaita bude wuta nan da nan. Kasar Sin kuma na son yin aiki tare da kasashen duniya wajen ci gaba da taka muhimmiyar rawa kan tabbatar da zaman karko da ci gaba da kuma wadata a kasar ta Sudan. (Mai fassara Bilkisu Xin)















Discussion about this post