A yau Talata, kasar Sin ta bayyana wasu matakai da nufin kara karfafa sayayya a kasuwannin gundumomi, tare da bunkasa yadda jama’a suke kashe kudi a yankunan, kamar yadda aka bayyana a wani wani tsari da ma’aikatar cinikayya ta fitar tare da wasu hukumomin gwamnati guda takwas.Tsarin ya yi kira da a inganta hanyoyin sayayya a gundumomi, ciki har da gyara cibiyoyin kasuwanci na garuruwa, da kasuwannin karkara da kuma bikin baje kolin kayayyaki na gida, da jawo hankulan kamfanonin cikin gida da na kasashen waje domin bude shagunan farko na matakin yankuna, da kuma karfafa sake bunkasa albarkatun kasa da ake da su.
Domin habaka sabbin tsare-tsaren kasuwanci, tsarin matakan zai tallafa wa kamfanoni da daidaikun ‘yan kasuwa da suka cancanta wajen bude shaguna da dama a karkashin lasisin kasuwanci daya a cikin gundumomi, yayin da kuma za a karfafa tallata shahararrun samfuran kayayyaki na cikin gida a kasuwannin matakin gunduma. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)














