Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya bayyana yadda ya ƙi amincewa da yunƙurin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi na zama mataimakinsa, yana mai cewa ya yi hakan ne saboda yana adawa da tikitin Muslim-Muslim domin kare muradun ƙasar.
Atiku ya bayyana hakan ne a cikin wata hira da aka yi da shi da harshen Hausa, wadda aka wallafa a shafin X, inda ya bayyana cewa wasu dattawan siyasa sun tuntube shi bayan ya samu tikitin takarar shugaban ƙasa, domin sanar da shi cewa Tinubu na son zama mataimakinsa.
A cewarsa, Tinubu ya tura wasu dattawa biyar domin su tattauna batun da shi, ciki har da Tom Ikimi, Bisi Akande da wasu mutum uku.
Atiku yace, “Ya ce zai mara mini baya wajen samun tikitin takara. Bayan na samu tikitin, sai ya tura dattawa biyar, daga cikinsu akwai Tom Ikimi, Bisi Akande da wasu uku. Sun gaya mini cewa Tinubu yana son ya zama mataimakina. Na gaya musu cewa, a matsayinsu na Kiristoci, ya kamata su fahimci cewa bai dace in zaɓi Musulmi ya zama mataimakina ba.
“Har na tambaye su dalilin da ya sa ba za su iya gaya masa hakan ba. Na gaya musu cewa ba zan iya amincewa da tikitin Muslim-Muslim ba, saboda hakan ba zai kasance cikin muradun ƙasarmu ba. Daga nan ya rabu da mu, ya mara wa marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua baya, Allah ya jiƙansa.”
Atiku ya ce tun daga wannan lokaci suka rabu da Tinubu, kuma ba su sake kasancewa a sansanin siyasa guda ba har sai a shekarar 2014, lokacin da ya shiga yakin neman zaɓen marigayi Muhammadu Buhari.














