Kasar Sin ta sake jaddada kira ga Japan da ta janye kalamanta na katobara da firaministar kasar Sanae Takaichi ta yi game da yankin Taiwan na kasar Sin, tare da nuna kwakkwarar niyya wajen kare ginshikin siyasa na dangantakar Sin da Japan ta hanyar daukar matakai na ainihi, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar ya bayyana a yau Litinin.
Mai magana da yawun, Lin Jian, ya furta hakan ne a taron manema labarai na yau da kullum, bayan jam’iyyun da ke mulki a gwamnatin hadaka ta Japan, watau Liberal Democratic Party da Japan Innovation Party, sun samu fiye da kashi biyu cikin uku na kujeru a majalisar wakilai bayan zaben gamagari na ranar Lahadi.
A yau Litinin, Sin ta kuma bukaci Japan ta yi tunani mai zurfi kan tarihinta na cin zarafi da ta yi wa wasu kasashe, tare da yin taka-tsantsan kan manyan batutuwa na tarihi kamar na gidan ibada na Yasukuni. Lin Jian ya bayyana haka a martanin da ya mayar game da kalaman da firaministar Japan Sanae Takaichi ta yi kwanan nan game da batun gidan ibada na Yasukuni.
Kazalika, dangane da hukuncin da babbar kotun yankin musamman na Hong Kong ta yanke wa Jimmy Lai a yau 9 ga watan Fabrairu, na daurin shekaru 20 a gidan yari kan tuhumetuhume biyu na gama kai da wasu daga waje da kuma wallafe-wallafen jaridu na tayar da bore. Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin, Lin Jian, ya fada a wannan rana cewa “Jimmy Lai shi ne babban mai tsarawa da kuma shiga dumu-dumu cikin jerin ayyukan nuna bore ga Sin da Hong Kong.”
Ya kara da cewa, aika-aikarsa sun yi matukar keta ka’idojin tsarin “kasa daya, mai amfani da tsarin mulki biyu,” sun kuma jefa tsaron kasa cikin babbar barazana, kana sun lalata samun wadata da kwanciyar hankalin Hong Kong da jin dadin jama’a kwarai da gaske. Dole ne a hukunta shi sosai bisa doka.”
Bugu da kari Lin Jian ya ce, “Jimmy Lai dan asalin kasar Sin ne. Muna kira ga kasashen da abin ya shafa da su girmama ‘yancin mulkin kai na kasar Sin, su girmama tsarin doka na Hong Kong, su kuma guji yin maganganu marasa kan-gado da suka shafi shari’ar da aka gudanar a yankin, tare da kauce wa tsoma baki cikin tsarin shari’ar Hong Kong ko harkokin cikin gidan Sin ta kowane irin salo.” (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post