Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun, ya bayyana cewa Sin tana bin hanyar samun ci gaba cikin lumana, kuma Sin ta habaka karfin soja ne don kare ikon mallakar kasa, tsaro, da muradun ci gaba, kana hakan ba shi da wata manufa a kan kowace kasa.
Guo ya bayyana haka ne a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Jumma’a.Dangane da bikin ranar yau a matsayin ranar “tsarin dokokin MDD”, Guo ya ce, Sin tana son yin aiki tare da kasashen duniya don inganta gina tsarin shugabanci na duniya mai adalci.
Dangane da girgizar kasar da ta faru a Venezuela, Guo ya ce gwamnatin Sin da kungiyar agaji ta Red Cross ta kasar za su samar da agajin gaggawa ga Venezuela.Bugu da kari, a cewar ma’aikatar harkokin wajen Sin, Liu Wei, manzon musamman na shugaban Sin Xi Jinping kuma ministan sufurin kasar, zai yi tafiya zuwa Victoria, babban birnin kasar Seychelles, domin halartar bikin cika shekaru 50 da samun ’yancin kai na Seychelles da za a gudanar a ranar 28 ga watan Yuni.(Safiyah Ma)














