Gwamnatin Tarayya ta bayyana cikakken bayanin yadda jami’an tsaron haɗin gwuiwa tsakanin Nijeriya da Jamhuriyar Nijar suka yi nasarar cafke manyan kwamandojin ƙungiyoyin ta’addanci na Boko Haram da ISWAP guda bakwai.
Ministan Tsaro na Jamhuriyar Nijar, Katambe Ibrahim, shi ne ya bayyana haka inda ya ce an kama manyan ‘yan ta’addan ne a Filin Jirgin Saman Umaru Musa Yar’adua da ke Jihar Katsina, daidai lokacin da suke ƙoƙarin dawowa gida bayan sun kammala aikin Hajji a ƙasar Saudiyya.
Ministan ya bayyana cewa wannan babban kamu ya faru ne sakamakon kyakkyawan shiri na musamman da musayar bayanan sirri na tsawon watanni tsakanin hukumomin tsaron ƙasashen biyu. Haka zalika, ya ƙara da cewa manyan kwamandojin na Boko Haram da ISWAP sun yi amfani da jabun fasfo da takardun bogi domin samun damar tafiya zuwa ƙasa mai tsarki, da nufin ɓoye ainihin fuskokinsu na ƴan ta’adda.
A cewar hukumomin tsaron, waɗanda aka kama ɗin jigo ne a cikin rukunonin da ke kitsa hare-hare, da samar da makamai, da kuma gudanar da dabarun yaƙi ga ƙungiyoyin ta’addan a yankunan tafkin Chadi da kuma iyakokin Nijeriya da Nijar. Jami’an tsaro sun daɗe suna bibiyar motsinsu, kuma kama su zai haddasa babban rauni ga tsarin shugabancin ƙungiyoyin a daidai lokacin da ake ƙarfafa tsaro a iyakokin ƙasashen biyu.
A halin yanzu, an tura waɗanda ake zargin zuwa babban sansanin bincike na sirri domin fuskantar tambayoyi masu zurfi, da nufin gano sauran mambobin rukuninsu da kuma hanyoyin da suke bi wajen samun kuɗaɗen shiga.
Gwamnatocin ƙasashen biyu sun jaddada cewa wannan nasara na nuna alfanun haɗin gwuiwar yanki wajen yaƙi da ta’addanci da kuma toshe duk wata kafa da masu laifi ke amfani da ita.














