ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

by Shehu Yahaya and Sulaiman
3 weeks ago
Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta ƙara ɗaukar sabbin matakai domin rage yawan haɗurran da ke faruwa a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe (western bypass) domin kare rayuwakar Al’umma masu amfani da hanyar.

A Wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatar yada labarai da Al’adu ta Jihar Kaduna ta shirya wanda aka tattaro shugabannin gargajiya, hukumomin tsaro, Hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) , kamfanonin da ke aikin hanyar da ƙungiyoyin direbobi, domin cimma matsaya kan yadda za’a kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da ingantaccen tsaro a kan hanyar.

An gudanar da taron ne ƙarƙashin jagorancin Sarkin Ruwan Zazzau, Alhaji Tahir Mahmoud, Hakimin Tudun Wada, inda mahalarta suka tattauna hanyoyin da za su taimaka wajen rage haɗurran da ke yawaita a kan wannan muhimmiyar hanya.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, wanda Babban Sakataren Ma’aikatar Iliya Duniya ya wakiltar, ya ce gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Sanata Uba Sani ta kafa kwamitin karta ta kwana domin tabbatar da rage yawan haɗurra a kan hanyar. Ya ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar duk wani mataki da zai tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Malam Ahmed Maiyaki ya kuma yaba da irin gudunmawar da sarakunan gargajiya da limamai ke bayarwa wajen wayar da kan jama’a da goyon bayan manufofin gwamnatin jihar na inganta tsaro da kiyaye doka a kan hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

A nasa jawabin, wakilin rukunin masana’antun Kamfanin Dangote Injiniya Jonathan Magoro, ya bayyana cewa ana sa ran kammala aikin babbar hanyar nan da watan Disamba, tare da sanya alamun rage gudu a wuraren da aka gano suna da haɗari domin rage afkuwar hatsarori.Yace sun samar da sabbin matakan rage hadura Akan hanyar wadanda suka hada da sanya alamun rage gudu da sanya ido wajen ganin masu amfani da hanyar suna bin dokoki yadda ya kamata. Suma Kamfanin Dantata wadanda aka suke kwangilar aikin hanyar sunce suna aiki kafaɗa da kafaɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya wajen tabbatar da nasarar aikin.

Sun bayyana cewa bayan kammala aikin za a girka fitilun kan titi, sannan an tantance wurare tara da ke da haɗari inda za a sanya alamun rage gudu.A nasa bangaren, Shugaban kungiyar masu manyan Motoci ta kasa (NARTO) rehsen jihar Kaduna Alhaji Babangida Ja’afar, ya yi kira ga masu amfani da hanya su guji ganganci, yana mai cewa tukin babbar mota ya bambanta da na ƙarama.

Ya buƙaci limamai da shugabannin gargajiya su ƙara wayar da kan jama’a kan bin dokokin hanya da kuma kaucewa daukar doka a hannunsu yayin da aka samu hadari. Ya kuma nuna damuwa kan yadda wasu ke ƙona manyan motocin da ke ɗauke da iskar gas ko man fetur bayan haddasa haɗari, cewa hakan na iya haddasa mummunar gobara da ƙarin asarar rayuka da dukiyoyi.

Haka kuma ya gargadi direbobin ƙananan motoci da su daina shiga gaban tireloli ba tare da isasshen tazara ba saboda hatsarin da hakan ke haifarwa.

Kungiyoyin masu babura masu ƙafa uku (Keke Napep) sun bayyana gamsuwarsu da matakan da gwamnatin Jihar Kaduna ke ɗauka domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe. Sun kuma yi alƙawarin haɗa kai da gwamnati wajen tabbatar da cikakken aiwatar da duk shawarwari da matakan da aka cimma a taron.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Majalisar Zartarwa Ta Jihar Kaduna Ta Amince Da Manufofin Haɓaka Walwalar Al’ummar Jihar
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15
Labarai

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Next Post
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.