ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

by Shehu Yahaya and Sulaiman
6 hours ago
Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta ƙara ɗaukar sabbin matakai domin rage yawan haɗurran da ke faruwa a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe (western bypass) domin kare rayuwakar Al’umma masu amfani da hanyar.

A Wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatar yada labarai da Al’adu ta Jihar Kaduna ta shirya wanda aka tattaro shugabannin gargajiya, hukumomin tsaro, Hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) , kamfanonin da ke aikin hanyar da ƙungiyoyin direbobi, domin cimma matsaya kan yadda za’a kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da ingantaccen tsaro a kan hanyar.

An gudanar da taron ne ƙarƙashin jagorancin Sarkin Ruwan Zazzau, Alhaji Tahir Mahmoud, Hakimin Tudun Wada, inda mahalarta suka tattauna hanyoyin da za su taimaka wajen rage haɗurran da ke yawaita a kan wannan muhimmiyar hanya.

ADVERTISEMENT

A jawabinsa, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, wanda Babban Sakataren Ma’aikatar Iliya Duniya ya wakiltar, ya ce gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Sanata Uba Sani ta kafa kwamitin karta ta kwana domin tabbatar da rage yawan haɗurra a kan hanyar. Ya ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar duk wani mataki da zai tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Malam Ahmed Maiyaki ya kuma yaba da irin gudunmawar da sarakunan gargajiya da limamai ke bayarwa wajen wayar da kan jama’a da goyon bayan manufofin gwamnatin jihar na inganta tsaro da kiyaye doka a kan hanyoyi.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

A nasa jawabin, wakilin rukunin masana’antun Kamfanin Dangote Injiniya Jonathan Magoro, ya bayyana cewa ana sa ran kammala aikin babbar hanyar nan da watan Disamba, tare da sanya alamun rage gudu a wuraren da aka gano suna da haɗari domin rage afkuwar hatsarori.Yace sun samar da sabbin matakan rage hadura Akan hanyar wadanda suka hada da sanya alamun rage gudu da sanya ido wajen ganin masu amfani da hanyar suna bin dokoki yadda ya kamata. Suma Kamfanin Dantata wadanda aka suke kwangilar aikin hanyar sunce suna aiki kafaɗa da kafaɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya wajen tabbatar da nasarar aikin.

Sun bayyana cewa bayan kammala aikin za a girka fitilun kan titi, sannan an tantance wurare tara da ke da haɗari inda za a sanya alamun rage gudu.A nasa bangaren, Shugaban kungiyar masu manyan Motoci ta kasa (NARTO) rehsen jihar Kaduna Alhaji Babangida Ja’afar, ya yi kira ga masu amfani da hanya su guji ganganci, yana mai cewa tukin babbar mota ya bambanta da na ƙarama.

Ya buƙaci limamai da shugabannin gargajiya su ƙara wayar da kan jama’a kan bin dokokin hanya da kuma kaucewa daukar doka a hannunsu yayin da aka samu hadari. Ya kuma nuna damuwa kan yadda wasu ke ƙona manyan motocin da ke ɗauke da iskar gas ko man fetur bayan haddasa haɗari, cewa hakan na iya haddasa mummunar gobara da ƙarin asarar rayuka da dukiyoyi.

Haka kuma ya gargadi direbobin ƙananan motoci da su daina shiga gaban tireloli ba tare da isasshen tazara ba saboda hatsarin da hakan ke haifarwa.

Kungiyoyin masu babura masu ƙafa uku (Keke Napep) sun bayyana gamsuwarsu da matakan da gwamnatin Jihar Kaduna ke ɗauka domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe. Sun kuma yi alƙawarin haɗa kai da gwamnati wajen tabbatar da cikakken aiwatar da duk shawarwari da matakan da aka cimma a taron.

Kaduna
Shehu Yahaya
+ posts Bio
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Matasa 1,200 Sun Amfana Da Horon Sana’o’i Ƙarƙashin Shirin ‘Renewed Hope’ A Kaduna
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Shehu Yahaya
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-yahaya/
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Kaduna
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa
  • Sulaiman
    Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”
  • Sulaiman
    Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

Tsohon Mataimakin Babban Sakataren MDD Ya Yaba Wa Dabarun Sin Kan Mulkin Kasa

June 26, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

June 26, 2026
Disu

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

Sin Ta Habaka Karfin Soja Ne Don Kare Ikon Mallakar Kasa Da Muradun Ci Gaba

June 26, 2026
Kaduna

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Amfani Da Haraji Ba Bisa Ka’ida Ba Ta Fakewa Da Zargin “Kwadagon Tilas”

June 26, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

An Fitar da Jadawalin Wasannin Zagayen Farko Na Gasar Carabao Cup ta 2026/2027

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

June 26, 2026
Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

Xi Ya Mika Jaje Kan Mummunar Girgizar Kasar Venezuela

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.