Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta ƙara ɗaukar sabbin matakai domin rage yawan haɗurran da ke faruwa a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe (western bypass) domin kare rayuwakar Al’umma masu amfani da hanyar.
A Wani taron masu ruwa da tsaki wanda ma’aikatar yada labarai da Al’adu ta Jihar Kaduna ta shirya wanda aka tattaro shugabannin gargajiya, hukumomin tsaro, Hukumar kiyaye hadura ta kasa (FRSC) , kamfanonin da ke aikin hanyar da ƙungiyoyin direbobi, domin cimma matsaya kan yadda za’a kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da ingantaccen tsaro a kan hanyar.
An gudanar da taron ne ƙarƙashin jagorancin Sarkin Ruwan Zazzau, Alhaji Tahir Mahmoud, Hakimin Tudun Wada, inda mahalarta suka tattauna hanyoyin da za su taimaka wajen rage haɗurran da ke yawaita a kan wannan muhimmiyar hanya.
A jawabinsa, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na Jihar Kaduna, Malam Ahmed Maiyaki, wanda Babban Sakataren Ma’aikatar Iliya Duniya ya wakiltar, ya ce gwamnatin jihar ƙarƙashin jagorancin Sanata Uba Sani ta kafa kwamitin karta ta kwana domin tabbatar da rage yawan haɗurra a kan hanyar. Ya ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen ɗaukar duk wani mataki da zai tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Malam Ahmed Maiyaki ya kuma yaba da irin gudunmawar da sarakunan gargajiya da limamai ke bayarwa wajen wayar da kan jama’a da goyon bayan manufofin gwamnatin jihar na inganta tsaro da kiyaye doka a kan hanyoyi.
A nasa jawabin, wakilin rukunin masana’antun Kamfanin Dangote Injiniya Jonathan Magoro, ya bayyana cewa ana sa ran kammala aikin babbar hanyar nan da watan Disamba, tare da sanya alamun rage gudu a wuraren da aka gano suna da haɗari domin rage afkuwar hatsarori.Yace sun samar da sabbin matakan rage hadura Akan hanyar wadanda suka hada da sanya alamun rage gudu da sanya ido wajen ganin masu amfani da hanyar suna bin dokoki yadda ya kamata. Suma Kamfanin Dantata wadanda aka suke kwangilar aikin hanyar sunce suna aiki kafaɗa da kafaɗa da masu riƙe da sarautun gargajiya wajen tabbatar da nasarar aikin.
Sun bayyana cewa bayan kammala aikin za a girka fitilun kan titi, sannan an tantance wurare tara da ke da haɗari inda za a sanya alamun rage gudu.A nasa bangaren, Shugaban kungiyar masu manyan Motoci ta kasa (NARTO) rehsen jihar Kaduna Alhaji Babangida Ja’afar, ya yi kira ga masu amfani da hanya su guji ganganci, yana mai cewa tukin babbar mota ya bambanta da na ƙarama.
Ya buƙaci limamai da shugabannin gargajiya su ƙara wayar da kan jama’a kan bin dokokin hanya da kuma kaucewa daukar doka a hannunsu yayin da aka samu hadari. Ya kuma nuna damuwa kan yadda wasu ke ƙona manyan motocin da ke ɗauke da iskar gas ko man fetur bayan haddasa haɗari, cewa hakan na iya haddasa mummunar gobara da ƙarin asarar rayuka da dukiyoyi.
Haka kuma ya gargadi direbobin ƙananan motoci da su daina shiga gaban tireloli ba tare da isasshen tazara ba saboda hatsarin da hakan ke haifarwa.
Kungiyoyin masu babura masu ƙafa uku (Keke Napep) sun bayyana gamsuwarsu da matakan da gwamnatin Jihar Kaduna ke ɗauka domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a a babbar hanyar Nnamdi Azikiwe. Sun kuma yi alƙawarin haɗa kai da gwamnati wajen tabbatar da cikakken aiwatar da duk shawarwari da matakan da aka cimma a taron.














