ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

by Abubakar Abba
10 hours ago
mai

Duk da rage farashin Man Fetur da Matatar Mai ta Ɗangote ta yi, har yanzu, dilalan Man a ƙasar nan, sun yi ƙememen rage farashin Man da suke sayarwa, masu ababen hawa, inda suke sayar da shi, kan tsohon farashi.

Matatar ta Ɗangote dai, ta rage farashin Man samfarin PMS, zuwa kan Naira  75, na kowacce Lita ɗaya, saɓanin yadda take sayarwa a baya, kan Naira 1, 250 zuwa Naira  1, 175, na kowacce Lita ɗaya.

A cewar Matatar ta Ɗangote, ta rage farashin Man ne, duba da cewa, yaƙin da ake yi, a Gabas ta Tsakya, ya ɗanyi sauƙi da kuma samun rauguwar farashin Ɗanyen Mai, a kasuwar duniya.

ADVERTISEMENT

Bugu da ƙari, Matatar ta ce, ta rage ne, farashin yin lodin Man zuwa Naira 100,575 na kowanne metric tan, wanda ta mayar da shi, daga Naira 1,595,790 zuwa Naira 1,495,215.

Wannan ragin farashin na Matatar ta Ɗangote dai, ana ganin zai ƙara haifar da wata sabuwar gasa a ɗaukacin kasuwannin da ake sayar da Man, a faɗin ƙasar.

LABARAI MASU NASABA

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Masu fashin baƙi a fannin, sun yi hasashen cewa, ragin ana kuma sa ran, zai faɗa kan Man Dizil nan da makwanni, masu zuwa, musamman idan aka ƙara samun raguwar farashinsa,  a kasuwar duniya, tare da ƙara daidaita, farashin Man Fetur.

Wannan sabon ragin farashin wanda ya fara aiki a ranar 16 ga watan Yunin 2026, bisa wani bincke da Jaridar LEADERSHIP ta gudanar, ya nuna cewa, wasu daga cikin manyan  dillan Man, sun rage farashin Man da suke sayarwa.

Bisa bincken da wakilinmu ya gudanar a wasu gidajen sayar da Man da ke a jihohin Legas Ogun, ya gano wani giɓi kan farashin Man Fetur da Man Dizil da gidajen, ke sayarwa.

Misali, a gidan Mani na MRS Filling, da ke a yankin Mowe na jihar  Ogun yabi sahun na Matatar Ɗangote, na rage farashin Man, inda yake sayarwa, kan Naira 1, 265, na kowacce Lita ɗaya.

Kazalika, a gidan Mai na NNPC da ke a yankin Ibafo, farashin Mai na PMS ana sayar da shi, kan Naira 1, 290 na kowacce Lita ɗaya.

Wasu daga cikin masu ababen hawa, sun koka kan yadda suke shan waya wajen sayen Man, inda wani Direba mai suna Mista Femi Adepoju, duk  lokacin da aka sayar da rage farashin Man a cikin gaggawa, su kan fara  bayyana  murnarsu, amma kuma daga baya, sai a ƙara mana farashin na Man.

mai
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026
Next Post
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.