Hukumar Kula da Yanayi ta Ƙasa (NiMet), ta shawarci ɗaukacin manoman ƙasar nan, kan cututtukan da ke harbin dabbobi a lokacin damina a hasashen ƙarin saukar ruwan sama a watan Yunin 2026, domin fara yin shuka a kan lokaci.
Kazalika, ta shawarci manoman da su ɗauki matakan kare gonakinsu daga afkuwar annobar ambaliyar ruwan sama da ƙwari da kuma cututtukan da ke lalata amfanin gona.
Wannan kiran na ƙunshe ne a cikin sanarwar hasashen da hukumar ta fitar a watan Yunin 2026, inda hukumar ta ce; a yanzu haka, an samu wadataccen ruwan sama a faɗin ƙasar, musamman a jihohi da dama da ke Arewacin ƙasar, wanda hakan ya sanya, akwai kyakkyawan yanayin da manoman ya kamata su duƙufa, domin fara yin shuka.
A cewar hukumar, jihohi kamar irin su Sakkwato, Kano, Jigawa, Kebbi, Zamfara, Katsina, Yobe da Borno, duba da tsarin saukar ruwan sama da suka samu, akwai buƙatar manoman jihohin su mayar da hankali wajen fara yin shuka.
NiMet ta ƙara da cewa, za a kuma samu saukar ruwan sama mai yawa a jihohi kamar su Edo, Delta, Bayelsa, Benue, Nasarawa, Taraba da wasu sassan Jihohin Filato, Kaduna, Yobe, Sakkwato, Kebbi, Borno da kuma Babban Birnin Tarayyar Abuja.
Hukumar ta ce, ruwan saman, zai taimaka wajen ƙara haɓaka shukar da aka yi, sai dai, ta yi gargaɗi cewa; ƙaruwar ruwan saman, zai iya jawo afkuwar ambaliyar ruwan sama, musamman a gonakin da ke daura da Kogi.
Domin kaucewa afkuwar annobar ta ambaliyar ruwan, hukumar ta shawarci manoman da su tabbatar da sun gyara hanyoyin ruwa da ke gonakinsu, domin su kare afkuwar ta annobar ambaliyar ruwan sama, musamman domin gujewa yin asara.
Bugu da ƙari, hukumar ta kuma shawarci masu kiwon dabbobi da su tabbatar sun samar da kyakkyawan guraren kwanan dabbobinsu, musamman domin kare su daga kamuwa da cututtuka.














