Gwamnatin tarayya, ta yunƙuro kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.
Wannan na zuwa ne, yayin da gwamnatin ta raba wa ƙananan manoma 2,930 buhunhunan takin zamani 11,720 a Abuja.
Hukumar samar da kuɗin tallafi ga manoma ta ƙasa (NADF) ce ta jagoranci rabar da takin, wanda aka ƙaddamar da rabonsa a Abuja.
A yayin ƙaddamarwar, ƙaramar ministar birnin, Mariya Mahmoud, ta jaddada ƙoƙarin gwamnatin, na cimma burin samar da wadataccen abinci a ƙasar, ta hanyar samar da ɗauki ga fannin.
Ta ce, wannan ɗaukin, zai taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar manoman da suka amfana da takin.
A cewarta, wannan ɗaukin, ya nuna irin mayar da hankalin da gwamnatin Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ke ci gaba da yi na ƙara ƙarfafa tsarin samar da wadataccen abinci da rage matsalolin da manoman ƙasar ke fuskanta a fannin.
Ta yi nuni da cewa, fannin aikin noma ne kan gaba, wajen haɓaka tattalin arzƙin ƙasar, wanda ta ce; tallafa wa manoman, wani ƙarin yunƙuri ne, na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.
Sannan ta yaba wa Shugaba Tinubu, musammamn kan ƙirƙiro da tsare-tsaren da suka taimaka, na samun rancen kuɗaɗen yin noma.
Ta buƙaci manoman da suka amfana da wannan tallafi, da su amfani da shi, yadda ya dace tare da kuma rungumar yin noma da kayan aiki na zamani, musamman domin su rinƙa yin girbi mai yawa.
Ministar ta bayar da tabbacin cewa, mahukuntan birnin, za su ci gaba da yin haɗaka da abokan haɗaka da sauran hukumomi da kuma masu ruwa da tsaki, domin samar da kayan aiki ga manoma da kuma horas da su.
A jawabinsa tun da farko, Shugaban Hukumar ta NADF, Injiniya Mohammed Ibrahim ya ce; wannan shirin ya nuna irin mayar da hakali da gwamnatin ke ci gaba da yi, na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da ƙara haɓaka tattalin arziƙin ƙasar.
Ya ce, ta hanyar aikin noma, ana iya samar da ayyukan yi wanda zai ƙara inganta rayuwar miliyoyin ƴan ƙasa.
Ibrahim ya ƙara da cewa, an tsara wannan shiri ne, domin tabbatar da an samar da ingantaccen takin ga manoman, musamman domin su tunkari noman kakar bana a cikin nasara.
Ya ci gaba da cewa, wannan ɗaukin, ana sa ran zai rage wa manoman tsadar aikin noma, wanda hakan zai ƙara ba su damar yin girbi mai matuƙar yawa.














