ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Raba Wa Manoma 2,930 Buhun Taki 11,720 A Abuja

by Abubakar Abba
9 hours ago
taki

Gwamnatin tarayya, ta yunƙuro kan ƙoƙarin da take ci gaba da yi na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Wannan na zuwa ne, yayin da gwamnatin ta raba wa ƙananan manoma 2,930 buhunhunan takin zamani 11,720 a Abuja.

Hukumar samar da kuɗin tallafi ga manoma ta ƙasa (NADF) ce ta jagoranci rabar da takin, wanda aka ƙaddamar da rabonsa a Abuja.

ADVERTISEMENT

A yayin ƙaddamarwar, ƙaramar ministar birnin, Mariya Mahmoud, ta jaddada ƙoƙarin gwamnatin, na cimma burin samar da wadataccen abinci a ƙasar, ta hanyar samar da ɗauki ga fannin.

Ta ce, wannan ɗaukin, zai taimaka matuƙa wajen inganta rayuwar manoman da suka amfana da takin.

LABARAI MASU NASABA

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

A cewarta, wannan ɗaukin, ya nuna irin mayar da hankalin da gwamnatin Shugaban Bola Ahmed Tinubu, ke ci gaba da yi na ƙara ƙarfafa tsarin samar da wadataccen abinci da rage matsalolin da manoman ƙasar ke fuskanta a fannin.

Ta yi nuni da cewa, fannin aikin noma ne kan gaba, wajen haɓaka tattalin arzƙin ƙasar, wanda ta ce; tallafa wa manoman, wani ƙarin yunƙuri ne, na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar.

Sannan ta yaba wa Shugaba Tinubu, musammamn kan ƙirƙiro da tsare-tsaren da suka taimaka, na samun rancen kuɗaɗen yin noma.

Ta buƙaci manoman da suka amfana da wannan tallafi, da su amfani da shi, yadda ya dace tare da kuma rungumar yin noma da kayan aiki na zamani, musamman domin su rinƙa yin girbi mai yawa.

Ministar ta bayar da tabbacin cewa, mahukuntan birnin, za su ci gaba da yin haɗaka da abokan haɗaka da sauran hukumomi da kuma masu ruwa da tsaki, domin samar da kayan aiki ga manoma da kuma horas da su.

A jawabinsa tun da farko, Shugaban Hukumar ta NADF, Injiniya Mohammed Ibrahim ya ce; wannan shirin ya nuna irin mayar da hakali da gwamnatin ke ci gaba da yi, na ƙara samar da wadataccen abinci a ƙasar da ƙara haɓaka tattalin arziƙin ƙasar.

Ya ce, ta hanyar aikin noma, ana iya samar da ayyukan yi wanda zai ƙara inganta rayuwar miliyoyin ƴan ƙasa.

Ibrahim ya ƙara da cewa, an tsara wannan shiri ne, domin tabbatar da an samar da ingantaccen takin ga manoman, musamman domin su tunkari noman kakar bana a cikin nasara.

Ya ci gaba da cewa, wannan ɗaukin, ana sa ran zai rage wa manoman tsadar aikin noma, wanda hakan zai ƙara ba su damar yin girbi mai matuƙar yawa.

taki
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kotu Ba Ta Da Hujjar Umartar INEC Ta Soke Rajistar Jam’iyyu —Uban Doman Lafiya

MASU ALAKA

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 
Noma Da Kiwo

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
taki
Noma Da Kiwo

Ku Gaggauta Fara Yin Shuka A Kakar Bana: Saƙon Hukumar NiMet Ga Manoma

June 27, 2026
taki
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Fara Aikin Gina Mayankar Zamani A Garin Jos

June 26, 2026
Next Post
taki

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.