ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
9 hours ago
yobe

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Yobe ta kama wata mace tare da wani da ake zargi da hannu wajen kisan gillat jaririyarta da aka haifa a Damaturu, inda rundunar ta bayyana lamarin a matsayin “mummuna da rashin imani.”

A cewar wata sanarwa da Kakakin Rundunar Ƴansandan Jihar, Dungus Abdulkarim ya fitar, an zargi matan ne da shaƙe jaririyar, sannan daga bisani suka ɓoye gawarta a cikin akwati tare da jefar da ita a bayan wani masallaci da ke rukunin gidaje na Anguwar Boka ta Damaturu.

Rundunar ta bayyana cewa jami’an sashen yaƙi da manyan laifuka (Ɓiolent Crime Response Unit) sun ɗauki mataki ne bayan samun kiran gaggawa ranar Talata game da zargin kisan jaririn da kuma ɓoye gawar tasa.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce: “Binciken farko ya nuna cewa wata mace da ake zargi, wadda ta haihu kwanan nan, ana zargin ta da hannu a wani lamari inda aka shaƙe jaririyar sannan aka ɓoye gawar a cikin akwati kafin a jefar da ita a bayan wani masallaci a yankin Anguwar Boka da ke Damaturu.”

Rundunar ta ƙara da cewa ɗaukar matakin gaggawa da ƴansanda suka yi ya kai ga kama mutum biyu waɗanda a halin yanzu ake gudanar da bincike a kansu.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

“Bayan ɗaukar matakin gaggawa na ƴansanda, an kama mutum biyu da ake zargi kuma a halin yanzu suna taimaka wa binciken. Ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin yayin da Rundunar ke ci gaba da tattara hujjoji domin ganin an yi adalci,” in ji Abdulkarim.

Allah wadai daga kwamishinan ƴansanda

Da yake mayar da martani kan lamarin, Kwamishinan Ƴansanda na Jihar Yobe, CP Usman Kanfani Jibrin, ya yi tir da wannan ɗanyen aiki, inda ya jaddada cewa kowane yaro yana da haƙƙin rayuwa, kariya, da mutunci ƙarƙashin doka.

“Rundunar ba za ta lamunci kowace irin tursasawa ko tashin hankali ga yara ko kowane mara kariya ba, kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi daidai da tsarin doka,” in ji Jibrin.

Rundunar ta sake jaddada cewa kowane yaro da aka haifa yana da wasu hakkoki na asali kuma ya cancanci kulawa, kariya, da mutunci, inda ta yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifin take waɗannan haƙƙoƙi zai fuskanci cikakken fushin doka.

Yunƙurin Sayar Da Jariri A Jihar Anambra

Wannan lamari yana zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan da jami’an Rundunar Ƴansanda ta Jihar Anambra suka daƙile yunƙurin wata budurwa ‘yar shekara 21 na sayar da jaririyarta a Igbariam, cikin Ƙaramar Hukumar Anambra ta Gabas.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar 22 ga watan Yuni, Rundunar Ƴansandan Anambra ta bayyana cewa jami’anta da ke ofishin Oyi sun yi aiki ne bisa sahihan bayanan sirri da suka samu ranar 19 ga watan Yuni, inda suka yi nasarar hana gudanar da wannan ciniki na miyagun mutane.

Sanarwar ta ce: “Jami’an ƴansanda sun gaggauta tsare uwar da jaririyarta tare da haɗa su da sauran mambobin iyalansu domin tabbatar da samun ingantacciyar kulawa, kariya, da goyon baya.”

Waɗannan abubuwa guda biyu da suka faru sun sake farfaɗo da fargaba game da laifukan da suka shafi jinjirai da ƙananan yara marasa kariya, yayin da hukumomin tsaro ke sake jaddada aniyarsu ta kare haƙƙin yara da tabbatar da cewa an hukunta masu laifi.

yobe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Bidiyo: Turji Ya Yi Iƙirarin Ɗaukar Alhakin Kashe Wasu Sojoji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

MASU ALAKA

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
Labarai

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
Manyan Labarai

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe
Labarai

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Next Post
yobe

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

LABARAI MASU NASABA

Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026
Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

Gasar Kofin Duniya: Senegal Ta Kai Zagaye Na 32 Bayan Lallasa Iraki Da Ci 5-0

June 27, 2026
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Sabuwar Dokar Shaidar Ɗan Ƙasa, Duba Abin Da Ta Ƙunsa

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.