Rundunar Ƴansanda ta Jihar Yobe ta kama wata mace tare da wani da ake zargi da hannu wajen kisan gillat jaririyarta da aka haifa a Damaturu, inda rundunar ta bayyana lamarin a matsayin “mummuna da rashin imani.”
A cewar wata sanarwa da Kakakin Rundunar Ƴansandan Jihar, Dungus Abdulkarim ya fitar, an zargi matan ne da shaƙe jaririyar, sannan daga bisani suka ɓoye gawarta a cikin akwati tare da jefar da ita a bayan wani masallaci da ke rukunin gidaje na Anguwar Boka ta Damaturu.
Rundunar ta bayyana cewa jami’an sashen yaƙi da manyan laifuka (Ɓiolent Crime Response Unit) sun ɗauki mataki ne bayan samun kiran gaggawa ranar Talata game da zargin kisan jaririn da kuma ɓoye gawar tasa.
Sanarwar ta ce: “Binciken farko ya nuna cewa wata mace da ake zargi, wadda ta haihu kwanan nan, ana zargin ta da hannu a wani lamari inda aka shaƙe jaririyar sannan aka ɓoye gawar a cikin akwati kafin a jefar da ita a bayan wani masallaci a yankin Anguwar Boka da ke Damaturu.”
Rundunar ta ƙara da cewa ɗaukar matakin gaggawa da ƴansanda suka yi ya kai ga kama mutum biyu waɗanda a halin yanzu ake gudanar da bincike a kansu.
“Bayan ɗaukar matakin gaggawa na ƴansanda, an kama mutum biyu da ake zargi kuma a halin yanzu suna taimaka wa binciken. Ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin yayin da Rundunar ke ci gaba da tattara hujjoji domin ganin an yi adalci,” in ji Abdulkarim.
Allah wadai daga kwamishinan ƴansanda
Da yake mayar da martani kan lamarin, Kwamishinan Ƴansanda na Jihar Yobe, CP Usman Kanfani Jibrin, ya yi tir da wannan ɗanyen aiki, inda ya jaddada cewa kowane yaro yana da haƙƙin rayuwa, kariya, da mutunci ƙarƙashin doka.
“Rundunar ba za ta lamunci kowace irin tursasawa ko tashin hankali ga yara ko kowane mara kariya ba, kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi daidai da tsarin doka,” in ji Jibrin.
Rundunar ta sake jaddada cewa kowane yaro da aka haifa yana da wasu hakkoki na asali kuma ya cancanci kulawa, kariya, da mutunci, inda ta yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifin take waɗannan haƙƙoƙi zai fuskanci cikakken fushin doka.
Yunƙurin Sayar Da Jariri A Jihar Anambra
Wannan lamari yana zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan da jami’an Rundunar Ƴansanda ta Jihar Anambra suka daƙile yunƙurin wata budurwa ‘yar shekara 21 na sayar da jaririyarta a Igbariam, cikin Ƙaramar Hukumar Anambra ta Gabas.
A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar 22 ga watan Yuni, Rundunar Ƴansandan Anambra ta bayyana cewa jami’anta da ke ofishin Oyi sun yi aiki ne bisa sahihan bayanan sirri da suka samu ranar 19 ga watan Yuni, inda suka yi nasarar hana gudanar da wannan ciniki na miyagun mutane.
Sanarwar ta ce: “Jami’an ƴansanda sun gaggauta tsare uwar da jaririyarta tare da haɗa su da sauran mambobin iyalansu domin tabbatar da samun ingantacciyar kulawa, kariya, da goyon baya.”
Waɗannan abubuwa guda biyu da suka faru sun sake farfaɗo da fargaba game da laifukan da suka shafi jinjirai da ƙananan yara marasa kariya, yayin da hukumomin tsaro ke sake jaddada aniyarsu ta kare haƙƙin yara da tabbatar da cewa an hukunta masu laifi.














