ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kama Uwa Da Abokiyar Burminta Kan Kisan Jariri A Jihar Yobe

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
yobe

Rundunar Ƴansanda ta Jihar Yobe ta kama wata mace tare da wani da ake zargi da hannu wajen kisan gillat jaririyarta da aka haifa a Damaturu, inda rundunar ta bayyana lamarin a matsayin “mummuna da rashin imani.”

A cewar wata sanarwa da Kakakin Rundunar Ƴansandan Jihar, Dungus Abdulkarim ya fitar, an zargi matan ne da shaƙe jaririyar, sannan daga bisani suka ɓoye gawarta a cikin akwati tare da jefar da ita a bayan wani masallaci da ke rukunin gidaje na Anguwar Boka ta Damaturu.

Rundunar ta bayyana cewa jami’an sashen yaƙi da manyan laifuka (Ɓiolent Crime Response Unit) sun ɗauki mataki ne bayan samun kiran gaggawa ranar Talata game da zargin kisan jaririn da kuma ɓoye gawar tasa.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ce: “Binciken farko ya nuna cewa wata mace da ake zargi, wadda ta haihu kwanan nan, ana zargin ta da hannu a wani lamari inda aka shaƙe jaririyar sannan aka ɓoye gawar a cikin akwati kafin a jefar da ita a bayan wani masallaci a yankin Anguwar Boka da ke Damaturu.”

Rundunar ta ƙara da cewa ɗaukar matakin gaggawa da ƴansanda suka yi ya kai ga kama mutum biyu waɗanda a halin yanzu ake gudanar da bincike a kansu.

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

“Bayan ɗaukar matakin gaggawa na ƴansanda, an kama mutum biyu da ake zargi kuma a halin yanzu suna taimaka wa binciken. Ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin yayin da Rundunar ke ci gaba da tattara hujjoji domin ganin an yi adalci,” in ji Abdulkarim.

Allah wadai daga kwamishinan ƴansanda

Da yake mayar da martani kan lamarin, Kwamishinan Ƴansanda na Jihar Yobe, CP Usman Kanfani Jibrin, ya yi tir da wannan ɗanyen aiki, inda ya jaddada cewa kowane yaro yana da haƙƙin rayuwa, kariya, da mutunci ƙarƙashin doka.

“Rundunar ba za ta lamunci kowace irin tursasawa ko tashin hankali ga yara ko kowane mara kariya ba, kuma duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi daidai da tsarin doka,” in ji Jibrin.

Rundunar ta sake jaddada cewa kowane yaro da aka haifa yana da wasu hakkoki na asali kuma ya cancanci kulawa, kariya, da mutunci, inda ta yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu da laifin take waɗannan haƙƙoƙi zai fuskanci cikakken fushin doka.

Yunƙurin Sayar Da Jariri A Jihar Anambra

Wannan lamari yana zuwa ne kwanaki ƙalilan bayan da jami’an Rundunar Ƴansanda ta Jihar Anambra suka daƙile yunƙurin wata budurwa ‘yar shekara 21 na sayar da jaririyarta a Igbariam, cikin Ƙaramar Hukumar Anambra ta Gabas.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar 22 ga watan Yuni, Rundunar Ƴansandan Anambra ta bayyana cewa jami’anta da ke ofishin Oyi sun yi aiki ne bisa sahihan bayanan sirri da suka samu ranar 19 ga watan Yuni, inda suka yi nasarar hana gudanar da wannan ciniki na miyagun mutane.

Sanarwar ta ce: “Jami’an ƴansanda sun gaggauta tsare uwar da jaririyarta tare da haɗa su da sauran mambobin iyalansu domin tabbatar da samun ingantacciyar kulawa, kariya, da goyon baya.”

Waɗannan abubuwa guda biyu da suka faru sun sake farfaɗo da fargaba game da laifukan da suka shafi jinjirai da ƙananan yara marasa kariya, yayin da hukumomin tsaro ke sake jaddada aniyarsu ta kare haƙƙin yara da tabbatar da cewa an hukunta masu laifi.

yobe
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

MASU ALAKA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
Labarai

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi
Manyan Labarai

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala
Labarai

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Next Post
yobe

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (1)

LABARAI MASU NASABA

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026
Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

Yawan Mu’amalar Kudi Tsakanin Mazauna Sin Da ’Yan Kasashen Waje Ya Hau Wani Sabon Matsayi A Tarihi

July 17, 2026
Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

Gasar Kofin Duniya: Da Ƙarfinmu Muka Kawo Matakin Da Muke Yanzu – Messi

July 17, 2026
Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

Matatar Man Dangote Ta Dawo Sayar Da Fetur A Dala

July 17, 2026
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Babban Taron AI Na Duniya Na 2026 Tare Da Gabatar Da Jawabi

July 17, 2026
Falalar Salatut Tasbihi

Falalar Salatut Tasbihi

July 17, 2026
A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

A Baya Ba A San Jihar Kano Da Harkar Daba Ba – Tsohon Shugaban NAHCON

July 17, 2026
Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.