ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Disu

Babban Sufeton Janar na  Ƴansandan Nijeriya, IGP Olatunji Disu, ya umarci ɗaukacin jami’ai maza da mata na Rundunar  (NPF) da su guji duk wani aiki na dandalin sada zumunta (social media) da ba su da izini a kai, wanda zai iya zubar da mutunci, ƙwarewa, da kuma kimar rundunar a idon jama’a.

Wata sanarwa da Kakakin Rundunar Ƴansandan Ƙasa (FPRO), CSP Anietie Okokon Iniedu ya fitar, ta bayyana cewa wannan umurni ya biyo bayan fargabar da ake da ita game da yadda jami’an ƴansanda ke ƙaruwa wajen ƙirƙira da wallafa bidiyoyi, gudanar da shirye-shiryen kai tsaye, da sauran ayyukan soshiyal midiya suna sanye da kayansanda, ko kuma a cikin wasu yanayi da ke nuna su a matsayin mambobin NPF ba tare da samun izini na hukuma ba.

Yana mai cewa: “IGP ya jaddada cewa, duk da cewa shafukan sada zumunta na zamani muhimmin makami ne na sadarwa da mu’amala da jama’a, amfani da su da jami’ai masu hidima za su yi dole ne ya kasance cikin tsarin dokoki, ka’idoji, da kuma Tsarin Manufofin Soshiyal Midiya na NPF.”

ADVERTISEMENT

Kakakin ya bayyana cewa Shugaban Ƴansandan ya lura da cewa: “An haramta wa jami’ai kirkira ko raba abubuwan da ba su da izini a kansu suna sanye da kayan sanda, yin tsokaci a gaban jama’a kan al’amuran yau da kullum na ƴansanda, bayyana bayanan sirri na ayyukan tsaro, ko amfani da matsayinsu na jami’an ƴansanda domin tallata kansu, nishaɗi, ko neman riba ta kasuwanci.”

“Domin tabbatar da bin wannan doka, an umarci Kwamishononin Ƴansanda, Shugabannin Ma’aikatu, Kwamandoji, da sauran jami’ai masu sanya ido da su gaggauta faɗakar da ma’aikata na ƙarƙashin umurninsu, sannan su tilasta bin wannan umurni baji-ba-gani.”

LABARAI MASU NASABA

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

“Za a gurfanar da jami’an sa ido kuma a gudanar da bincike a kansu idan suka gaza ɗaukar matakin da ya dace kan duk wani saɓa doka da aka samu a yankunansu na kulawa.”

Haka zalika, CSP Iniedu ya ƙara da cewa: “IGP ya ƙara umartar Sashen Leƙen Asiri na Rundunar (FID) da Sashen Kula da Ƙa’idojin Ƙwarewa (Ɗ-Sƙuad) da su ƙarfafa sanya ido kan dandalolin sada zumunta na zamani, domin gano jami’an da ke gudanar da ayyukan da suka saɓa wa ƙa’idojin ƙwarewa na NPF.”

A cewar Kakakin rundunar (FPRO): “NPF tana jaddada aniyarta na tabbatar da ɗa’a, ƙwarewa, da kuma riƙon amana wajen sadarwa da jama’a, tare da tabbatar wa mambobin al’umma ci gaba da sadaukarwarta wajen kiyaye amincewar jama’a da kuma mutuncin hukumar.”

Disu
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
Kotu Da Ɗansanda

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Next Post
Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A  Titin Bypass

Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Sabbin Matakan Dakile Haɗura A Titin Bypass

LABARAI MASU NASABA

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.