Babban Sufeton Janar na Ƴansandan Nijeriya, IGP Olatunji Disu, ya umarci ɗaukacin jami’ai maza da mata na Rundunar (NPF) da su guji duk wani aiki na dandalin sada zumunta (social media) da ba su da izini a kai, wanda zai iya zubar da mutunci, ƙwarewa, da kuma kimar rundunar a idon jama’a.
Wata sanarwa da Kakakin Rundunar Ƴansandan Ƙasa (FPRO), CSP Anietie Okokon Iniedu ya fitar, ta bayyana cewa wannan umurni ya biyo bayan fargabar da ake da ita game da yadda jami’an ƴansanda ke ƙaruwa wajen ƙirƙira da wallafa bidiyoyi, gudanar da shirye-shiryen kai tsaye, da sauran ayyukan soshiyal midiya suna sanye da kayansanda, ko kuma a cikin wasu yanayi da ke nuna su a matsayin mambobin NPF ba tare da samun izini na hukuma ba.
Yana mai cewa: “IGP ya jaddada cewa, duk da cewa shafukan sada zumunta na zamani muhimmin makami ne na sadarwa da mu’amala da jama’a, amfani da su da jami’ai masu hidima za su yi dole ne ya kasance cikin tsarin dokoki, ka’idoji, da kuma Tsarin Manufofin Soshiyal Midiya na NPF.”
Kakakin ya bayyana cewa Shugaban Ƴansandan ya lura da cewa: “An haramta wa jami’ai kirkira ko raba abubuwan da ba su da izini a kansu suna sanye da kayan sanda, yin tsokaci a gaban jama’a kan al’amuran yau da kullum na ƴansanda, bayyana bayanan sirri na ayyukan tsaro, ko amfani da matsayinsu na jami’an ƴansanda domin tallata kansu, nishaɗi, ko neman riba ta kasuwanci.”
“Domin tabbatar da bin wannan doka, an umarci Kwamishononin Ƴansanda, Shugabannin Ma’aikatu, Kwamandoji, da sauran jami’ai masu sanya ido da su gaggauta faɗakar da ma’aikata na ƙarƙashin umurninsu, sannan su tilasta bin wannan umurni baji-ba-gani.”
“Za a gurfanar da jami’an sa ido kuma a gudanar da bincike a kansu idan suka gaza ɗaukar matakin da ya dace kan duk wani saɓa doka da aka samu a yankunansu na kulawa.”
Haka zalika, CSP Iniedu ya ƙara da cewa: “IGP ya ƙara umartar Sashen Leƙen Asiri na Rundunar (FID) da Sashen Kula da Ƙa’idojin Ƙwarewa (Ɗ-Sƙuad) da su ƙarfafa sanya ido kan dandalolin sada zumunta na zamani, domin gano jami’an da ke gudanar da ayyukan da suka saɓa wa ƙa’idojin ƙwarewa na NPF.”
A cewar Kakakin rundunar (FPRO): “NPF tana jaddada aniyarta na tabbatar da ɗa’a, ƙwarewa, da kuma riƙon amana wajen sadarwa da jama’a, tare da tabbatar wa mambobin al’umma ci gaba da sadaukarwarta wajen kiyaye amincewar jama’a da kuma mutuncin hukumar.”














