ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Shugaban Jam’iyyar PRP na ƙasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana fargaba kan yadda yanayin siyasar ƙasar ke ƙara tsananta, inda ya yi gargaɗin cewa jam’iyyun adawa a Nijeriya suna rayuwa cikin tsoron yiwuwar soke rajistarsu.

Yayin da yake jawabi a cikin wani shiri na gidan talabijin na Channels TV, Baba-Ahmed ya bayyana cewa abubuwan da ke faruwa a fagen siyasa da kuma hukunce-hukuncen kotu na baya-bayan nan sun ƙara jefa makomar jam’iyyun adawa cikin rashin tabbas.

Lokacin da aka tambaye shi ko jam’iyyarsa ta PRP tana tsoron soke rajistar, Baba-Ahmed ya amsa da cewa babu wata jam’iyyar adawa da ke kwana da idanuwanta biyu a rufe a halin yanzu, in ban da jam’iyyar APC mai mulki. Ya jaddada cewa kowace jam’iyyar adawa da ke da’awar cewa tana cikin kwanciyar hankali, to kuwa ba ta ɗauki harkar siyasar ƙasar da gaske ba, duba da yadda hukuncin Babbar Kotun Tarayya ta Lokoja ya soke rajistar jam’iyyar NDC a cikin makon nan.

ADVERTISEMENT

Baya ga batun rajista, Baba-Ahmed ya taɓo batun tsaron ƙasa, inda ya soki yunkurin gwamnatin tarayya na samar da ‘yansandan jihohi (state police). Ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kwashe shekaru uku tana jan kafa kan batun, kuma samar da su ba tare da an gyara tsarin rundunar ‘yansandan tarayya da sojoji ba, zai ƙara dagula matsalolin tsaron ƙasar ne kawai tare da ba wa gwamnoni damar yin abin da suka ga dama.

A ƙarshe, shugaban na PRP ya jaddada cewa akwai abubuwa da dama da Shugaba Tinubu zai iya yi da jami’an tsaron da ke ƙasa a halin yanzu domin kawo ƙarshen garkuwa da mutane da kashe-kashen da ke faruwa.

LABARAI MASU NASABA

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Game da tarihin jam’iyyar PRP kuwa, ya ƙaryata iƙirarin cewa jam’iyyar ta samo asali ne daga marigayi Firimiyan Arewa, Sir Ahmadu Bello Sardauna, inda ya bayyana cewa a can baya ma jam’iyyar ta kasance ƙaya ce a jikin gwamnatin Sardaunan saboda adawa da siyasarsa.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano
  • Abubakar Sulaiman
    Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure
  • Abubakar Sulaiman
    Sabon Tsarin Tikitin Abinci Na Nusuk Zai Iya Ƙara Kuɗin Bizar Umrah
  • Abubakar Sulaiman
    Direba Ya Hallaka Ɗalibar Jami’ar Kiwon Lafiya Ta Azare, Ya Gudu

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Next Post
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.