Shugaban Jam’iyyar PRP na ƙasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana fargaba kan yadda yanayin siyasar ƙasar ke ƙara tsananta, inda ya yi gargaɗin cewa jam’iyyun adawa a Nijeriya suna rayuwa cikin tsoron yiwuwar soke rajistarsu.
Yayin da yake jawabi a cikin wani shiri na gidan talabijin na Channels TV, Baba-Ahmed ya bayyana cewa abubuwan da ke faruwa a fagen siyasa da kuma hukunce-hukuncen kotu na baya-bayan nan sun ƙara jefa makomar jam’iyyun adawa cikin rashin tabbas.
Lokacin da aka tambaye shi ko jam’iyyarsa ta PRP tana tsoron soke rajistar, Baba-Ahmed ya amsa da cewa babu wata jam’iyyar adawa da ke kwana da idanuwanta biyu a rufe a halin yanzu, in ban da jam’iyyar APC mai mulki. Ya jaddada cewa kowace jam’iyyar adawa da ke da’awar cewa tana cikin kwanciyar hankali, to kuwa ba ta ɗauki harkar siyasar ƙasar da gaske ba, duba da yadda hukuncin Babbar Kotun Tarayya ta Lokoja ya soke rajistar jam’iyyar NDC a cikin makon nan.
Baya ga batun rajista, Baba-Ahmed ya taɓo batun tsaron ƙasa, inda ya soki yunkurin gwamnatin tarayya na samar da ‘yansandan jihohi (state police). Ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kwashe shekaru uku tana jan kafa kan batun, kuma samar da su ba tare da an gyara tsarin rundunar ‘yansandan tarayya da sojoji ba, zai ƙara dagula matsalolin tsaron ƙasar ne kawai tare da ba wa gwamnoni damar yin abin da suka ga dama.
A ƙarshe, shugaban na PRP ya jaddada cewa akwai abubuwa da dama da Shugaba Tinubu zai iya yi da jami’an tsaron da ke ƙasa a halin yanzu domin kawo ƙarshen garkuwa da mutane da kashe-kashen da ke faruwa.
Game da tarihin jam’iyyar PRP kuwa, ya ƙaryata iƙirarin cewa jam’iyyar ta samo asali ne daga marigayi Firimiyan Arewa, Sir Ahmadu Bello Sardauna, inda ya bayyana cewa a can baya ma jam’iyyar ta kasance ƙaya ce a jikin gwamnatin Sardaunan saboda adawa da siyasarsa.














