ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 28, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Adawa Na Cikin Tsoron Soke Rajistarsu – Baba-Ahmed

by Abubakar Sulaiman
1 day ago

Shugaban Jam’iyyar PRP na ƙasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana fargaba kan yadda yanayin siyasar ƙasar ke ƙara tsananta, inda ya yi gargaɗin cewa jam’iyyun adawa a Nijeriya suna rayuwa cikin tsoron yiwuwar soke rajistarsu.

Yayin da yake jawabi a cikin wani shiri na gidan talabijin na Channels TV, Baba-Ahmed ya bayyana cewa abubuwan da ke faruwa a fagen siyasa da kuma hukunce-hukuncen kotu na baya-bayan nan sun ƙara jefa makomar jam’iyyun adawa cikin rashin tabbas.

Lokacin da aka tambaye shi ko jam’iyyarsa ta PRP tana tsoron soke rajistar, Baba-Ahmed ya amsa da cewa babu wata jam’iyyar adawa da ke kwana da idanuwanta biyu a rufe a halin yanzu, in ban da jam’iyyar APC mai mulki. Ya jaddada cewa kowace jam’iyyar adawa da ke da’awar cewa tana cikin kwanciyar hankali, to kuwa ba ta ɗauki harkar siyasar ƙasar da gaske ba, duba da yadda hukuncin Babbar Kotun Tarayya ta Lokoja ya soke rajistar jam’iyyar NDC a cikin makon nan.

ADVERTISEMENT

Baya ga batun rajista, Baba-Ahmed ya taɓo batun tsaron ƙasa, inda ya soki yunkurin gwamnatin tarayya na samar da ‘yansandan jihohi (state police). Ya bayyana cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kwashe shekaru uku tana jan kafa kan batun, kuma samar da su ba tare da an gyara tsarin rundunar ‘yansandan tarayya da sojoji ba, zai ƙara dagula matsalolin tsaron ƙasar ne kawai tare da ba wa gwamnoni damar yin abin da suka ga dama.

A ƙarshe, shugaban na PRP ya jaddada cewa akwai abubuwa da dama da Shugaba Tinubu zai iya yi da jami’an tsaron da ke ƙasa a halin yanzu domin kawo ƙarshen garkuwa da mutane da kashe-kashen da ke faruwa.

LABARAI MASU NASABA

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

Game da tarihin jam’iyyar PRP kuwa, ya ƙaryata iƙirarin cewa jam’iyyar ta samo asali ne daga marigayi Firimiyan Arewa, Sir Ahmadu Bello Sardauna, inda ya bayyana cewa a can baya ma jam’iyyar ta kasance ƙaya ce a jikin gwamnatin Sardaunan saboda adawa da siyasarsa.

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya
  • Abubakar Sulaiman
    TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu
  • Abubakar Sulaiman
    Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

MASU ALAKA

Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya
Manyan Labarai

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe
Siyasa

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta
Manyan Labarai

NDC Ta Ce Za Ta Ɗaukaka Ƙara Kan Hukuncin Soke Rajistarta

June 26, 2026
Next Post
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026
Husaini Isa Ya Gargaɗi Ƴan Takarar NDC A Kano Kan Buƙatar Kiyaye Ƙa’dojin Jam’iyya

Hukuncin Kotun Lokoja Kan NDC Barazana Ce Ga Dimokuraɗiyya — Ameh

June 28, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai

El-Rufai Ya Shafe Fiye Da Kwanaki 125 A Garƙame

June 28, 2026
Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

Ghana Ta Soke Lasisin Mallakar Bindiga Da Aka Bai Wa Fararen Hula A Baya

June 28, 2026
Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

June 27, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Jaddada Cewa Ba Ta Da Wani Shiri Na Bada Damar Binciken Wuraren Nukiliyarta

June 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sin Ta Karu Da Kashi 18.8% Cikin Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 27, 2026
Yaushe Za A Gane Kungiyar Da Za Ta Lashe Gasar Premier?

An Raba Jadawalin Gasar Premier Ta Ingila Ta Kakar Wasan 2026/2027

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.