Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Sun Lei, ya yi jawabi bayan da kwamitin sulhun MDD ya kada kuri’a kan daftarin tsawaita wa’adin takunkumin da aka kakabawa kasar Sudan ta Kudu a jiya Juma’a, inda ya kalubalanci kwamitin sulhun da ya gyara, ko soke takunkumin idan akwai damar hakan, ta yadda za a magance matsin lamba, da tsoma baki cikin harkokin kasar ta cikin gida ta hanyar saka mata takunkumin.
Sun Lei ya bayyana cewa, an kada kuri’u kan tsawaita wa’adin daftarin ne, ba wai gyara abubuwan dake cikin daftarin ba, amma takunkumin da aka sakawa kasar Sudan ta Kudu na baya, ya haifar wa kasar matsin lamba, kuma babu adalci a bayanan daftarin, don haka kasar Sin ba ta nuna cikakkiyar amincewa da wasu sassan daftarin ba, maimakon hakan ta janye jiki daga jefa kuri’ar. Kwamitin sulhun ya ayyana hana shigar da makamai kasar Sudan ta Kudu a tsawon shekaru kimanin 8, lamarin da ya haifar da cikas ga gwamnatin Sudan ta Kudun wajen bayar da kariya ga jama’a, da kiyaye zaman lafiya a kasar.
A bangarenta kuwa, kasar Sin tana da ra’ayin cewa, takunkumin turba ce ta daidaita matsalar, amma ba shi ne zai warware matsalar ba, don haka ya kamata kwamitin sulhun ya taimakawa kasar da ake batu a kanta ta nemi soke takunkumin.
Kwamitin sulhun MDD ya zartas da kudurin a jiya Juma’a, mai kunshe da tsawaita wa’adin takunkumin hana shigar da makamai, da sauran matakai da aka gindayawa kasar Sudan ta Kudu da karin shakara daya, wato har zuwa ranar 31 ga watan Mayun shekarar 2027. Kudurin ya samu kuri’un amincewa guda 9, kana sassa 6 sun ki jefa kuri’unsu, amma duk da haka daga karshe an zartas da shi. (Zainab Zhang)















Discussion about this post