Kasar Sin ta bukaci Amurka da Tarayyar Turai da su daina kururuta abin da ake kira da wai batun kabilu, sannan su daina tsoma baki a harkokin cikin gida na kasar Sin, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun, ya bayyana a yau Jumma’a.
A cewar rahotannin kafofin watsa labarai, Amurka da Tarayyar Turai sun bayyana abin da ake kira da wai ‘damuwa game da dokar karfafa hadin kan kabilu da ci gabansu ta kasar Sin’, wadda ta fara aiki a ranar Larabar da ta gabata.
A martanin da ya mayar, Guo ya shaida wa taron manema labarai na yau da kullum cewa, ta hanyar daukar ra’ayi na son zuciya da kuma bata manufofin harkokin kabilu na kasar Sin da gangan, kasashen da abin ya shafa sun kirkiri tare da yada labarun kanzon kurege, da yin katsalandan a harkokin cikin gidan Sin, da kuma yin kafar ungulu ga hadin kan kabilun kasar Sin. Inda Guo ya kara da cewa, “Kasar Sin tana adawa da wannan sosai”.
Da yake mayar da martani game da kalaman firaministan Indiya, Narendra Modi, cewa Indiya da Japan za su karfafa hadin gwiwa a fannin ma’adanai masu muhimmanci, Guo Jiakun ya bayyana cewa, bai kamata a kulla irin wannan hadin gwiwa da nufin wani ba ko kuma kawo cikas ga muradunsa.Ya ce, kamata ya yi hadin gwiwa tsakanin kasashe ya taimaka wajen inganta fahimta da amincewa tsakanin kasashen yanki da kuma kare zaman lafiya da kwanciyar hankali na yanki. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














