Daga CGTN Hausa0Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce matakin Amurka na toshe tashoshin ruwan kasar Iran na da matukar hadari, kuma hakan rashin sanin ya kamata ne.
Guo, ya bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, lokacin da yake amsa tambaya mai nasaba da matakin dakarun sojin Amurka na fara datse jiragen ruwa, masu shige da fice a tashoshin ruwan Iran.
Jami’in ya kara da cewa, Sin na kira ga dukkanin sassa, da su yi biyayya ga yarjejeniyar tsagaita wuta, su rungumi shawarwari da tattaunawar zaman lafiya, kana su aiwatar da matakai na hakika na sassauta yanayin matsi da ake fuskanta, da dawowa zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigin Hormuz ba tare da bata lokaci ba.Guo, ya ce idan har Amurka ta nace sai ta kakaba karin harajin fito kan kasar Sin, ta fakewa da zargin “Fitar da kayayyakin aikin soji”, ita ma a nata bangare Sin za ta dauki matakan mayar da martani.
Ya ce duk wasu rahotanni dake cewa wai Sin na samar da tallafin kayan soji ga Iran, karairayi ne kawai da ake kitsawa.
Daga nan sai ya bayyana matsayar Sin, ta yin taka-tsantsan da sanin ya kamata, dangane da fitar da kayayyakin aikin soji zuwa ketare, tare da kayyade su bisa dokokin fitar da su na cikin gida, da ka’idoji, da sauke nauyin dake wuyan kasar na cudanyar kasa da kasa. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post