Hukumar kula da ayyukan sama jannati ta kasar Sin, ta sanar a yau cewa, an zabi wasu ‘yan kasar Pakistan biyu a matsayin ‘yan sama jannati na kasar waje na farko, da za su karbi horo domin shiga aikin binciken sararin samaniya na Sin, inda ta kira shi a matsayin gagarumar nasarar hadin gwiwar kasa da kasa game da binciken sararin samaniya ta Sin.
Cikin wata sanarwa da ta fitar, hukumar ta ce Muhammad Zeeshan Ali da Khurram Daud za su zo Sin nan ba da dadewa ba, a matsayin wadanda za a bai wa horo da za a iya turawa binciken sararin samaniya.
Bayan sun kammala horo da tantancewa, daya daga cikinsu zai shiga cikin tawagar masu aikin binciken sararin samaniya na Sin, wanda zai zama dan sama jannati na farko na kasar waje da zai shiga tashar Tiangong ta kasar Sin.Hukumar ta ce a farkon watan Afrilu aka kammala zaben baki ‘yan sama jannati na shirin binciken sararin samaniyar na kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Msutapha)















Discussion about this post