Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Guo Jiakun ya bayyana cewa, dangantakar diflomasiyya tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka ta taka muhimmiyar rawa ga kyautatuwar dangantakar kasashen biyu, bangaren Sin yana maraba da ziyarar shugaban Amurka Donald Trump a Sin.
Guo ya bayyana hakan ne yayin da yake amsa tambayar da wani dan jarida ya yi masa game da kalaman da shugaba Trump ya yi gabanin ziyararsa a kasar Sin, a gun taron manema labarai na yau da kullum da aka gudanar yau Laraba.
Dangane da barkewar gagarumar zanga-zangar adawa da yaki mafi girma a Japan a cikin shekaru da dama da suka gabata kuwa, Guo ya bayyana cewa, wannan yana nuna cewa, mutane daga dukkanin sassan rayuwa a Japan suna kara fahimtar cewa, komawa kan turbar nuna karfin soja, hanya ce da ba za ta bulle ba. (Safiyah Ma)















Discussion about this post