ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kama Tsohuwa Mai Shekaru 65 Bisa Zargin Safarar Ƙwayoyi Ga Ƴan Boko Haram

by Abubakar Sulaiman
8 months ago
Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Sojojin Rundunar Haɗin Gwuiwa ta Arewa maso Gabas, Operation HAƊIN KAI, sun kama wata mata mai shekaru 65, Hauwa Abulazeez, bisa zargin samar da haramtattun ƙwayoyi ga ƴan Boko Haram da ke aiki a wasu sassan Jihar Borno. Kamen ya gudana ne a ranar 23 ga Janairu, 2026, a ƙaramar hukumar Askira Uba, bayan samun sahihan bayanan sirri, a cewar wata sanarwa da kakakin rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba, ya fitar.

Sanarwar ta bayyana Hauwa a matsayin “ɗaya daga cikin manyan masu samar da tabar wiwi (cannabis sativa) ga ƴan ta’adda,” tana kuma rarraba kayan a yankunan Askira Uba da makwabtan ƙauyuka kamar Rumirgo, da Gwahi, da Wamdiyo, da Uvu da Gaya. Rundunar ta ce ana kallon ta a matsayin muhimmin ginshiƙi a da’irar masu safarar haramtattun ƙwayoyi a faɗin waɗannan al’ummomi.

  • Sojoji Sun Kashe Shugaban ‘Yan Ta’adda Munzir, Sun Kama Wasu 34 A Borno
  • Sojoji Sun Hallaka Kwamandojin Boko Haram 2, Sun Kama Wasu 8 A Borno

Binciken farko ya nuna cewa ana zargin Hauwa na samo ƙwayoyin ne daga ƙaramar hukumar Sarti Baruwa a Jihar Taraba, sannan tana bi ta hanyoyin da aka riga aka tanada wajen shigar da su zuwa Borno domin rarrabawa. A yayin aikin da aka gudanar ƙarƙashin Operation Desert Sanity V, Sojoji sun ƙwato buhuna 14 na tabar wiwi da aka matse, masu nauyin kimanin kilo 30 gaba ɗaya.

ADVERTISEMENT

Rundunar ta ce ana ci gaba da tsare wadda ake zargi domin zurfafa bincike, tare da bin sawun sauran mutanen da ke cikin wannan hanyar safarar ƙwayoyi. Ta jaddada cewa katse hanyoyin samar da haramtattun kayab zai taimaka wajen rage ƙarfin ayyukan ta’addanci, tare da ƙara tsaro da tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin Arewa maso Gabas.

Sojoji
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote
  • Abubakar Sulaiman
    Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Sojoji Sun Ceto Yarinya Ƴar Shekara 13, Sun Hallaka Ƴan Ta’adda A Dajin Zamfara

Sojoji Sun Ceto Yarinya Ƴar Shekara 13, Sun Hallaka Ƴan Ta’adda A Dajin Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Sojoji

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.