ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 6 Tare Da Kama Wasu A Filato

by Sulaiman
3 years ago
Sojoji

Dakarun sojojin rundunar Operation Safe Haven (OPSH), sun kashe wasu masu garkuwa da mutane shida tare da kama wasu ‘yan bindiga a wasu ayyuka daban-daban a Filato da wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna.

 

Rundunar, ta kuma ce, an kama mutane 54 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da garkuwa da mutane, barna a gonakin jama’a, fashi da makami, kera bindiga da safarar miyagun kwayoyi da dai sauransu.

ADVERTISEMENT
  • 4 Daga Cikin Masallatan Da ‘Yan Bindiga Suka Kashe A Kaduna Sun Bar Marayu Da Zawarawa 61

Jami’in yada labarai na rundunar, Kyaftin Oya James, a wata sanarwa da ya fitar, ya ce, sojojin sun kuma kama wasu masu garkuwa da mutane guda uku da kuma wani da ake zargin dan bindiga ne mai suna Dauda Tahiru kan harin baya-bayan nan na karshe da aka kai a kauyen Heipang da ke karamar hukumar Barkin Ladi ta jihar Filato.

 

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

“Hakazalika, bayan samun bayanan sirri, sojojin sun gano tare da kama wani shahararren mai kera bindiga wanda ake kira da Nyam, da wani kuma a kauyukan Kwang/Kafanchan na Jos ta Kudu da Jema’a na jihohin Filato da Kaduna.

 

A yayin samamen, sojojin sun kwato bindiga kirar AK-47 guda daya, harsashi mai tsawon 7.62mm guda 55, bindiga kirar DICON AK-47 guda daya mai lamba 563706042 da kuma kwalbasar harsashi guda daya.

 

James ya kara da cewa, sojojin sun kama wasu makiyaya biyu Musa Mamuda da Musa Alhaji da laifin lalata gonaki a kauyen Yagbak da ke Zangon Kataf sannan kuma an kwato shanu 27 a karamar hukumar Bokkos ta jihar Filato.

 

Ya kara da cewa, an kama wasu dilolin kwayoyi 41 a Kongo Rasha da ke Jos ta Arewa, an tsare su domin hukumar NDLEA ta ci gaba da gudanar da bincike akansu.

Sojoji
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI
  • Sulaiman
    Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

MASU ALAKA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’
Tsaro

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft
Labarai

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Next Post
Zaɓe: Jobe Ya Liƙa Dan Ganduje Da Ƙasa A Kotu

Zaɓe: Jobe Ya Liƙa Dan Ganduje Da Ƙasa A Kotu

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa ONSA Kan Shirin Horon Masu Tsaron Daji ‘Forest Guards’

July 9, 2026
Auto Draft

TCN Ta Kammala Gyaran Layin Wutar Lantarkin Zaria–Funtua 132kV

July 9, 2026
Auto Draft

DSS Ta Kama ‘Yar Jarida Zainab Sodiq Kan Zargin Mallakar Drone Ba Tare da Cikakkun Takardu ba

July 9, 2026
Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji

July 9, 2026
Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

Shaidar EFCC Ya Ce Sirika Bai Sanya Hannu A Takardun Kwangilar Naira Biliyan 2 Ba

July 9, 2026
’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.