Ɗan wasan gaba na tawagar Faransa, Ousmane Dembélé, ya ce sukar da ake yi wa abokin wasansa Kylian Mbappé ta wuce gona da iri, musamman bayan tauraron na Real Madrid ya fuskanci matsin lamba sakamakon rashin kyan wasan ƙungiyar.
Dembélé ya shaida wa jaridar Marca cewa ana yi wa Mbappé rashin adalci, yana mai cewa mutane sun wuce gona da iri wajen sukar sa saboda kawai shi Mbappé ne. Ya ce Mbappé babban ɗan wasa ne kuma mutum ne nagari a wajen fili, don haka bai kamata a rika bibiyarsa kan kowane ƙaramin abu ba.
Ya ƙara da cewa duk da matsin lambar da yake fuskanta a kulob ɗinsa, Mbappé na taka muhimmiyar rawa a tawagar Faransa, inda ya bayyana shi a matsayin jagora mai tasiri a cikin ƙungiyar.
Faransa za ta fara gasar Kofin Duniya ne da ƙarawa da ƙasar Senegal ranar Talata, yayin da ake sa ran wannan gasar za ta kasance ta ƙarshe ga koci Didier Deschamps, inda ake alaƙanta Zinedine Zidane da maye gurbinsa nan gaba.















Discussion about this post