ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 month ago
NPA

Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA) da Birtaniya sun sake tabbatar da aniyarsu ta kara karfafa hadin gwiwa a harkokin ruwa, tare da mayar da hankali kan binciken taswirar ruwa, tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa, bunkasa tashoshin jiragen ruwa da kuma gina kwarewar ma’aikata.

Hakan ya biyo bayan wata ziyarar girmamawa da Mataimakin Babban Kwamishinan Birtaniya a Nijeriya, Jonny Badter, Babban Jami’in Hydrographer na Birtaniya, Angus Essenhigh, da jami’an Ofishin Hydrographic na Birtaniya (UKHO) suka kai wa Manajan Daraktan NPA.

Tawagar ta samu tarba daga Manajan Daraktan NPA, Abubakar Dantsoho, tare da Daraktan Zartarwa mai kula da Injiniya da Ayyukan Fasaha da sauran manyan jami’an hukumar.

ADVERTISEMENT

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun tattauna hanyoyin kara karfafa dadaddiyar hadin gwiwar da ke tsakanin Nijeriya da Birtaniya a harkokin ruwa, musamman a fannoni masu muhimmanci ga tsaron zirga-zirga a ruwa, ingancin ayyukan tashoshin jiragen ruwa da kuma ci gaba mai dorewa a fannin.

Da yake jawabi, Dantsoho ya bayyana shirye-shiryen zamanantar da tashoshin jiragen ruwa da NPA ke aiwatarwa domin mayar da tashoshin Nijeriya cibiyoyin kasuwanci masu gogayya a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

Ya bayyana cewa hukumar na zuba jari a manyan ayyuka da suka hada da gyaran tashoshin jiragen ruwa, inganta hanyoyin ruwa da kuma sabunta muhimman kayayyakin more rayuwa domin kara ingancin aiki, rage lokacin da jiragen ruwa ke dauka a tashoshi da kuma karfafa matsayin Nijeriya a kasuwancin ruwa na yanki da na duniya.

Tattaunawar ta kuma mayar da hankali kan bunkasa kwarewar binciken taswirar ruwa domin inganta tsaro a zirga-zirgar ruwa da kuma saukaka ayyukan tashoshin jiragen ruwa a hanyoyin ruwan Nijeriya.

Tawagar Birtaniya ta sake jaddada aniyarta ta tallafa wa ci gaban wannan fanni a Nijeriya ta hanyar hadin gwiwar fasaha da musayar ilimi.

Ganawar ta sake nuna kakkarfan dangantakar diflomasiyya da ke tsakanin Nijeriya da Birtaniya, da kuma jajircewarsu wajen bunkasa kirkire-kirkire, habaka kwarewa da ci gaba mai dorewa a masana’antar harkokin ruwa.

NPA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Majalisa Ta Yi Watsi Da Bukatar MDD Ta Bincikar Badakalar Satar Daliban Oyo

MASU ALAKA

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC
Tattalin Arziki

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa
Tattalin Arziki

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Next Post
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa - Peter Obi

LABARAI MASU NASABA

NPA

Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu

July 25, 2026
Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

Yadda Jami’an Tsaro Suka Fatattaki ’Yan Ta’adda A Wasu Jihohin Nijeriya, Sun Kama ‘Yan Kasar Pakistan Bakwai

July 25, 2026
NPA

Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

July 25, 2026
Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

Manufofin Tattalin Arzikin Gwamnatin Tinubu Sun Lalata Rayukan Al’ummar Nijeriya —ADC

July 25, 2026
An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.