ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
1 hour ago
NPA

Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA) da Birtaniya sun sake tabbatar da aniyarsu ta kara karfafa hadin gwiwa a harkokin ruwa, tare da mayar da hankali kan binciken taswirar ruwa, tsaron zirga-zirgar jiragen ruwa, bunkasa tashoshin jiragen ruwa da kuma gina kwarewar ma’aikata.

Hakan ya biyo bayan wata ziyarar girmamawa da Mataimakin Babban Kwamishinan Birtaniya a Nijeriya, Jonny Badter, Babban Jami’in Hydrographer na Birtaniya, Angus Essenhigh, da jami’an Ofishin Hydrographic na Birtaniya (UKHO) suka kai wa Manajan Daraktan NPA.

Tawagar ta samu tarba daga Manajan Daraktan NPA, Abubakar Dantsoho, tare da Daraktan Zartarwa mai kula da Injiniya da Ayyukan Fasaha da sauran manyan jami’an hukumar.

ADVERTISEMENT

A yayin ganawar, bangarorin biyu sun tattauna hanyoyin kara karfafa dadaddiyar hadin gwiwar da ke tsakanin Nijeriya da Birtaniya a harkokin ruwa, musamman a fannoni masu muhimmanci ga tsaron zirga-zirga a ruwa, ingancin ayyukan tashoshin jiragen ruwa da kuma ci gaba mai dorewa a fannin.

Da yake jawabi, Dantsoho ya bayyana shirye-shiryen zamanantar da tashoshin jiragen ruwa da NPA ke aiwatarwa domin mayar da tashoshin Nijeriya cibiyoyin kasuwanci masu gogayya a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

Ya bayyana cewa hukumar na zuba jari a manyan ayyuka da suka hada da gyaran tashoshin jiragen ruwa, inganta hanyoyin ruwa da kuma sabunta muhimman kayayyakin more rayuwa domin kara ingancin aiki, rage lokacin da jiragen ruwa ke dauka a tashoshi da kuma karfafa matsayin Nijeriya a kasuwancin ruwa na yanki da na duniya.

Tattaunawar ta kuma mayar da hankali kan bunkasa kwarewar binciken taswirar ruwa domin inganta tsaro a zirga-zirgar ruwa da kuma saukaka ayyukan tashoshin jiragen ruwa a hanyoyin ruwan Nijeriya.

Tawagar Birtaniya ta sake jaddada aniyarta ta tallafa wa ci gaban wannan fanni a Nijeriya ta hanyar hadin gwiwar fasaha da musayar ilimi.

Ganawar ta sake nuna kakkarfan dangantakar diflomasiyya da ke tsakanin Nijeriya da Birtaniya, da kuma jajircewarsu wajen bunkasa kirkire-kirkire, habaka kwarewa da ci gaba mai dorewa a masana’antar harkokin ruwa.

NPA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Samar Da Abinci:Jihar Nasarawa Ta Fara Shirin Gina Kananan Madatsun Ruwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ba Zai Yiwu A Cimma Yarjejeniya Ba Tare Da Sanya Batun Lebanon Ba —Iran

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe
Tattalin Arziki

Darajar Naira Ta Sauka A Kasuwar Musayar Kuɗaɗe

June 6, 2026
Next Post
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa - Peter Obi

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.