An kammala taron ministocin cinikayya na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ta kasashen Asiya da Pasifik (APEC) ranar Asabar a birnin Suzhou na Sin, inda dukkan bangarori suka amince da Sanarwar Suzhou da Taswirar Bunkasa Masana’antar Samar da Hidimomi, lamarin da zai bayar da muhimmiyar gudunmuwar nasarorin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ga taron shugabannin kungiyar da za a yi nan gaba a bana.
A matsayinta na muhimmiyar mamba cikin kungiyar kasashen APEC, kasar Sin ta kasance mai shiga ana damawa da ita yadda ya kamata a fannoni daban-daban na harkokin kungiyar.
Yayin taron ministocin kula da cinikayya na kasashen kungiyar APEC, Sin ta bukaci a inganta tsarin dunkule tattalin arzikin yankin da kara daukaka tsarin cinikayya tsakanin bangarori daban-daban da karfafa tuntuba da tattaunawa a bangarori masu tasowa.
Sakamakon taron ya amince da shawarwarin da Sin ta gabatar, wadanda ba karawa hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya ta APEC kuzari kadai zai yi ba, har da nuna niyyar Sin da hakkin da ke wuyanta na inganta raya tattalin arzikin Asiya da tekun Pasifik da ma na duniya baki daya, daga sabbin nasarorin da ake samu daga tafarkin zamanantar da kasar Sin. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post