Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su ci gaba da kare dimokuraɗiyya tare da rungumar haɗin kai, yayin da ƙasar ke bikin cika shekaru 27 na mulkin farar hula ba tare da katsewa ba. .
A jawabin Ranar Dimokuraɗiyya na 12 ga Yuni, Tinubu ya ce duk da ƙalubalen da ake fuskanta, dimokuraɗiyyar Nijeriya na ci gaba da ƙarfi kuma wajibi ne a ƙara inganta ta.
Shugaban ya taɓo batun tsaro, inda ya ce gwamnatinsa ta ɗauki matakai masu tsauri wajen yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da ‘yan bindiga.
A cewarsa, an ware Naira tiriliyan 5.41 a kasafin 2026 domin tsaro, tare da ɗaukar sabbin jami’an ‘yansanda sama da 50,000 da ƙarin sojoji domin ƙarfafa tsaron ƙasa.
A ɓangaren tattalin arziƙi, shugaba Tinubu ya kare sauye-sauyen da gwamnatinsa ke aiwatarwa, yana mai cewa sun taimaka wajen daidaita tattalin arziƙi, da ƙara kuɗaɗen shiga ga jihohi da ƙananan hukumomi, da kuma dawo da ƙwarin gwuiwar masu zuba jari. Ya kuma ce ƙarfin tace mai a cikin gida ya ƙaru, yayin da gwamnati ke ƙoƙarin rage hauhawar farashi da samar da ayyukan yi.
Tinubu ya karrama jaruman gwagwarmayar June 12 da sauran masu fafutukar dimokuraɗiyya, yana mai cewa babbar girmamawa gare su shi ne gina Nijeriya mai adalci, da tsaro da wadata. Ya jaddada cewa al’ummar Nijeriya na iya fuskantar ƙalubale, amma ba za su taɓa karaya ba.















Discussion about this post