ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ne Ya Haifar Da Matsalolin Tsaro A Arewa – Gwamnan Jigawa

by Sadiq
6 months ago
Talauci

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya ce talauci ne babban dalilin da ya haifar da matsalolin a Arewa.

Ya bayyana haka ne a Kaduna lokacin bikin cika shekaru 25 da kafa Ƙungiyar Arewa Consultative Forum (ACF).

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Dandalin Kasuwancin Makamashi Na Sin Da Rasha
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kare Nasarar Yakin Duniya Na II

Wannan ya fito ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar.

ADVERTISEMENT

Gwamna Namadi ya ce ko da yake matsalar tsaro babbar barazana ce, dole a magance tushen matsalar, musamman talauci, ta hanyar amfani da tsare-tsaren tattalin arziƙi na dogon lokaci.

Ya bayyana cewa Arewa tana da albarkatun ƙasa, ƙasar noma, da ɗimbin ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Don haka, akwai damar kawar da talauci ta hanyar bunƙasa harkar noma.

A cewarsa, yawancin matsalolin tsaro suna da nasaba da talauci, kuma Arewa ba ta da hujjar ci gaba da kasancewa cikin talauci kasancewar tana da albarkatu da dama.

Saboda haka ne shugabannin Arewa ke himmatuwa wajen inganta noma.

Gwamnan ya yi imanin cewa gyare-gyaren da ACF, Gwamnonin Arewa, da Gwamnatin Tarayya ke goyon baya za su taimaka wajen sauya tsarin noma da farfaɗo da tattalin arziƙin yankin.

Ya ƙara da cewa bunƙasa noma zai samar da ayyukan yi da hanyoyin dogaro da kai ga miliyoyin mutane, kuma wajibi ne shugabanni su haɗa kai domin cimma wannan buri.

Gwamna Namadi ya taya ACF murna bisa cika shekaru 25 da kafuwa, sannan ya yaba da rawar da ta ke takawa wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba a Arewa da Nijeriya baki ɗaya.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Ronaldo Zai Iya Buga Wasan Farko Na Kofin Duniya Bayan Hukuncin FIFA

Ronaldo Zai Iya Buga Wasan Farko Na Kofin Duniya Bayan Hukuncin FIFA

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.