ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Talauci Ne Ya Haifar Da Matsalolin Tsaro A Arewa – Gwamnan Jigawa

by Sadiq
10 months ago
Talauci

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya ce talauci ne babban dalilin da ya haifar da matsalolin a Arewa.

Ya bayyana haka ne a Kaduna lokacin bikin cika shekaru 25 da kafa Ƙungiyar Arewa Consultative Forum (ACF).

  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Dandalin Kasuwancin Makamashi Na Sin Da Rasha
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Kare Nasarar Yakin Duniya Na II

Wannan ya fito ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar.

ADVERTISEMENT

Gwamna Namadi ya ce ko da yake matsalar tsaro babbar barazana ce, dole a magance tushen matsalar, musamman talauci, ta hanyar amfani da tsare-tsaren tattalin arziƙi na dogon lokaci.

Ya bayyana cewa Arewa tana da albarkatun ƙasa, ƙasar noma, da ɗimbin ma’aikata.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Don haka, akwai damar kawar da talauci ta hanyar bunƙasa harkar noma.

A cewarsa, yawancin matsalolin tsaro suna da nasaba da talauci, kuma Arewa ba ta da hujjar ci gaba da kasancewa cikin talauci kasancewar tana da albarkatu da dama.

Saboda haka ne shugabannin Arewa ke himmatuwa wajen inganta noma.

Gwamnan ya yi imanin cewa gyare-gyaren da ACF, Gwamnonin Arewa, da Gwamnatin Tarayya ke goyon baya za su taimaka wajen sauya tsarin noma da farfaɗo da tattalin arziƙin yankin.

Ya ƙara da cewa bunƙasa noma zai samar da ayyukan yi da hanyoyin dogaro da kai ga miliyoyin mutane, kuma wajibi ne shugabanni su haɗa kai domin cimma wannan buri.

Gwamna Namadi ya taya ACF murna bisa cika shekaru 25 da kafuwa, sannan ya yaba da rawar da ta ke takawa wajen inganta zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaba a Arewa da Nijeriya baki ɗaya.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Ronaldo Zai Iya Buga Wasan Farko Na Kofin Duniya Bayan Hukuncin FIFA

Ronaldo Zai Iya Buga Wasan Farko Na Kofin Duniya Bayan Hukuncin FIFA

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.