ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Kawar Da Harajin Kwastam Na Sin Ga Kasashen Afirka

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 month ago
Sin

A shekarun baya bayan nan dangantakar Sin da kasashen Afirka na kara kyautata, tare da fuskantar sauyi mai na-garta, irin sauyin da ke nuni ga zurfafar fannonin tattalin arziki da ma yadda Sin ke kara kyautata manufofinta na bude kofa.

Cikin tsawon shekaru, alaka tsakanin Sin da kasashen Afirka ta fi shafar gina ababen more rayuwa: irinsu layin dogo, da manyan hanyoyin mota, da tashoshin jiragen ruwa, da na samar da lantarki da sauransu.

Amma a baya bayan nan, musamman cikin shekarar nan ta 2026, mun ga yadda aka samu wani sabon ci gaba, wato matakin da Sin ta aiwatar na kawar da dukkannin harajin kwastam, kan hajojin kasashen Afirka masu dangantakar diflomasiyya da kasar wadanda ake shigarwa babbar kasuwar kasar ta Sin.

ADVERTISEMENT

Karkashin wannan babbar manufa, Sin na fadada matakan dunkule fannin hada-hadar cinikayya, da raya masana’antu tare da kasashen Afirka, kari kan matakin samar da kudaden gudanar da manyan ayyukan raya kasashen nahiyar.

Tasirin wannan manufa ta kawar da haraji ya shafi rage shingayen cinikayya, da baiwa hajojin Afirka karin dama, ta dunkulewa cikin tsarin rarraba hajoji na duniya mai alaka da Sin.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Ta wannan hanya, Sin na ingiza ikon kasashen Afirka, na yin hadin gwiwar bunkasa masana’antu da sarrafa hajoji, da fadada sayayya, da yayata fasahohin ci gaba na Sin a sassan nahiyar, wanda hakan kari ne kan fannin fitar da kayayyakin sarrafawa na ma’adanai da sauransu da sassan biyu suka jima suna cin gajiyarsa.

Ga kasashen Afirka, wannan ci gaba zai dace da burikansu na bunkasa a dogon lokaci, ta yadda za su kara cin gajiya daga fifikonsu a fannin samar da albarkatu, da rage dogaro da fitar da hajojin da ba a sarrafa ba a gida.

Bugu da kari, kasashen Afirka za su kara samun damammaki irin wadanda a baya babu su gwargwadon yadda gwamnatocinsu suka iya tsara manufofi a cikin gida, da ikonsu na aiwatar da matakan cin gajiyar wannan manufa ta kawar da haraji cikin tsawon lokaci nan gaba. (Saminu Alhassan)

Sin
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya
  • Sulaiman
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    Ƙa’idojin Gudanar Da Biyan Kuɗi Nan Take Domin Kare Kai Daga Zamba
  • Sulaiman
    Falalar Yawaita Tuba Ga Ubangiji (Istigfari)
Sin
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

MASU ALAKA

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji
Daga Birnin Sin

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Next Post
Abubuwa 4 Da Ke Jagorantar Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa: Bijirewa Fito Na Fito

Abubuwa 4 Da Ke Jagorantar Sabon Salon Dangantakar Kasa Da Kasa: Bijirewa Fito Na Fito

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.