A shekarun baya bayan nan dangantakar Sin da kasashen Afirka na kara kyautata, tare da fuskantar sauyi mai na-garta, irin sauyin da ke nuni ga zurfafar fannonin tattalin arziki da ma yadda Sin ke kara kyautata manufofinta na bude kofa.
Cikin tsawon shekaru, alaka tsakanin Sin da kasashen Afirka ta fi shafar gina ababen more rayuwa: irinsu layin dogo, da manyan hanyoyin mota, da tashoshin jiragen ruwa, da na samar da lantarki da sauransu.
Amma a baya bayan nan, musamman cikin shekarar nan ta 2026, mun ga yadda aka samu wani sabon ci gaba, wato matakin da Sin ta aiwatar na kawar da dukkannin harajin kwastam, kan hajojin kasashen Afirka masu dangantakar diflomasiyya da kasar wadanda ake shigarwa babbar kasuwar kasar ta Sin.
Karkashin wannan babbar manufa, Sin na fadada matakan dunkule fannin hada-hadar cinikayya, da raya masana’antu tare da kasashen Afirka, kari kan matakin samar da kudaden gudanar da manyan ayyukan raya kasashen nahiyar.
Tasirin wannan manufa ta kawar da haraji ya shafi rage shingayen cinikayya, da baiwa hajojin Afirka karin dama, ta dunkulewa cikin tsarin rarraba hajoji na duniya mai alaka da Sin.
Ta wannan hanya, Sin na ingiza ikon kasashen Afirka, na yin hadin gwiwar bunkasa masana’antu da sarrafa hajoji, da fadada sayayya, da yayata fasahohin ci gaba na Sin a sassan nahiyar, wanda hakan kari ne kan fannin fitar da kayayyakin sarrafawa na ma’adanai da sauransu da sassan biyu suka jima suna cin gajiyarsa.
Ga kasashen Afirka, wannan ci gaba zai dace da burikansu na bunkasa a dogon lokaci, ta yadda za su kara cin gajiya daga fifikonsu a fannin samar da albarkatu, da rage dogaro da fitar da hajojin da ba a sarrafa ba a gida.
Bugu da kari, kasashen Afirka za su kara samun damammaki irin wadanda a baya babu su gwargwadon yadda gwamnatocinsu suka iya tsara manufofi a cikin gida, da ikonsu na aiwatar da matakan cin gajiyar wannan manufa ta kawar da haraji cikin tsawon lokaci nan gaba. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post