Tawagar likitocin kasar Sin ta 14 mai aiki a kasar Ghana, da hadin gwiwar Sin da asibitin kawance na Lekma, sun shirya kwas na inganta kwarewar aiki a fannin aikin tiyata ta zamani ga likitocin tiyata na Ghana.
A jiya Litinin ne aka kaddamar da horon a birnin Accra fadar mulkin kasar. Da yake tsokaci game da hakan, shugaban tawagar likitocin kasar ta Sin Yang Yongguang, ya ce horon zai karkata ne ga koyar da aikin fida ta amfani da kankanin yanka a jiki, da aikin yanar ido, ta yadda za a samar da dandalin musayar ilimi da kwarewa mai dorewa, yayin da ake yayata fasahohi masu nasaba da hakan a kasar ta Ghana.
Yang Yongguang, ya ce da tallafin tawagar likitocin kasar Sin, asibitin Lekma ya cimma nasarar gudanar da tiyatar ta zamani da aikin yanar ido, akasari a karon farko a Ghana da ma sassan yammacin Afirka.
Ya ce bisa hadin gwiwar kwazon dukkanin bangarorin, matsayin asibitin Lekma ya karu daga babbar cibiyar kiwon lafiya, zuwa cibiyar kula da lafiya ta shiyya da ta fita daban, bisa fifikonta na iya gudanar da aikin tiyata ta amfani da mafi kankantar yanka a jiki, da aikin yanar ido. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post