Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Shugaba Bola Tinubu yana aiki tuƙuru don magance matsalolin tsaro a Nijeriya.
Ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi ƙwararru daga Kwalejin Nazarin Tsaro ta Ƙasa (NISS) a ofishinsa, waɗanda suka zo domin gabatar da rahoton karatunsu.
- Sojoji Ba Za Su Iya Kawo Ƙarshen ‘Yan Bindiga Ba, Gwamnati Ta Yi Sulhu Da Su – Sheikh Gumi
- An Gudanar Da Taro Na 3 Na Kasashen Sin Da Iran Da Saudiyya
Shettima, ya ce gwamnati na da niyyar ci gaba da tallafa wa jami’an tsaro domin su iya kare ƙasar yadda ya kamata.
Ya ƙara da cewa dole ne kowa ya haɗa kai don inganta tsaro a Nijeriya da ma Afirka baki ɗaya.
Shugaban NISS, Joseph Odama, ya bayyana cewa manyan jami’ai 78 sun kammala shirin horo na tsawon watanni 10, ciki har da masu zuwa daga wasu ƙasashen Afirka guda biyar.
Ya ce an horar da su yadda za su yi tunani cikin hikima su kuma samo mafita game da matsalolin tsaro.
Ƙungiyar ta miƙa rahoto da ke ba da shawarar ƙarin haɗin kai da ƙarfafa dokoki domin magance matsalolin tsaro a Nijeriya da Afirka.














