ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Kai Ziyarar Aiki Netherlands Da Saudiyya 

by Sadiq
2 years ago
Tinubu

Shugaba Bola Tinubu zai halarci taron tattalin arzikin duniya da aka shirya gudanarwa a ranakun 28 zuwa 29 ga watan Afrilu a birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

A wata sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale, ya fitar a ranar Litinin, ya ce, “Bisa gayyatar da Firaministan Netherlands, Mark Rutte ya yi masa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 A Kasuwa A Zamfara
  • Sojoji Sun Lalata Masana’antar Sarrafa Burodin ‘Yan Ta’adda A Borno

Yayin ziyarar, shugaba Tinubu zai tattauna da Firaministan, sannan zai shiga taruka daban-daban tare da Mai Martaba, Sarki Willem-Alexander da Sarauniya Maxima ta Masarautar.

ADVERTISEMENT

“Yayin da yake kasar Netherlands, shugaba Tinubu zai halarci taron kasuwanci da zuba jari a tsakanin Nijeriya da Netherlands wanda zai hada shugabannin kungiyoyi a kasashen biyu don gano damarmaki na hadin gwiwa, musamman a fannin noma da kula da ruwa wajen samar da sabbin hanyoyin samar da mafita mai dorewa ga ayyukan noma.

“Za a kuma tattauna da jami’an kasar game da ayyukan sarrafa tashar jiragen ruwa wadanda a duniya an san su da kwarewa a kai.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

“Bayan tafiyarsa Netherlands, shugaban zai ci gaba da halartar wani taro na musamman na tattalin arzikin duniya (WEF) wanda aka shirya gudanarwa a ranakun 28-29 ga Afrilu a Riyadh, Saudiyya.

“A taron tattalin arzikin duniya, wanda ya mayar da hankali kan Haɗin gwiwar Duniya, Ci gaba da Makamashi don Ci gaba, Shugaba Tinubu da mukarrabansa za su yi amfani da damar taron na sama da shugabanni 1,000 daga ‘yan kasuwa, gwamnati, da jami’o’in ilimi don shiga tattaunawa don ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci.”

Shugaba Tinubu zai samu rakiyar wasu ministoci da wasu manyan jami’an gwamnatinsa.

A baya dai Tinubu ya halarci irin wannan taro a Saudiyya, inda ya gana da masu ruwa da tsaki don neman su zuba hannun jari a Nijeriya.

MASU ALAKA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata
Manyan Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi
Manyan Labarai

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami
Manyan Labarai

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Next Post
Mayakan Boko Haram 2 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

Mayakan Boko Haram 2 Sun Mika Wuya Ga Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

Mutane 15 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsarin Mota, 17 Sun Jikkata

July 6, 2026
Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

Hukuncin Kisa Ne Ya Dace Da Ƴan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Gagdi

July 6, 2026
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Kwace Kadarori 57 Na Tsohon Minista Malami

July 6, 2026
Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

Ƴan Bindiga Sun Kashe Manoma 9, Sun Sace Da Dama A Birnin Gwari

July 6, 2026
Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

Gwamnatin Kano Ta Kashe Biliyan 928 A Ayyukan Ci Gaba 1,508

July 6, 2026
Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

Jonathan Ya Musanta Zargin Tayin Naira Biliyan 500 Domin Raba Kuri’un Kudu Maso Kudu

July 6, 2026
FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.