ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Zabi Mai Shekaru 39 A Matsayin Mataimakinsa

by Sadiq
2 years ago
Trump

Tsohon Shugaban Amurka, Donald Trump ya zabi Sanata James David Vance na Jihar Ohio, a matsayin mataimakinsa a takarar shugaban kasa karkashin jam’iyyar Republican.

A ranar Litinin Trump mai shekaru 78 ya zabi Vance mai shekaru 39 a matsayin abokin tafiyarsa a zaben 2024 wanda za a yi a ranar 5 ga watan Nuwamba.

  • Sin Ta Fadada Manufar Yada Zango A Kasar Ba Tare Da Biza Ba Zuwa Karin Tashoshi
  • Tsadar Rayuwa: Gwamnatin Tarayya Ta Fara Rabon Tirelolin Shinkafa 740 A Fadin Nijeriya 

Baya ga shi Vance, a baya, an bayyana mutum biyu da ake tunanin Trump zai dauka ciki har da Sanata Marco Rubio na Jihar Florida da gwamnan Jihar North Dakota Doug Burgum.

ADVERTISEMENT

Trump, ya sanar da zabinsa da aka jima ana dako a babban taron jam’iyyar Republican na kasa da aka fara a Milwaukee da ke Jihar Winsconsin.

Dukkanin wakilan da suka halarci babban taron na ‘yan Republican daga jihohin Amurka sun jaddada Trump a matsayin dan takararsu a zaben shugaban kasa, inda ya samu wakilai sama da 1,215 adadin da ake bukata dan takara ya samu.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Gangamin na ‘yan Republican na zuwa ne kwanaki biyu bayan da Trump ya tsallake rijiya da baya inda wani dan bindiga ya yi yunkurin hallaka shi yayin gangamin yakin neman zabe a Pennsylvania a ranar Asabar.

An haifi Vance ne a garin Middleton da ke Jihar Ohio a ranar 2 ga watan Agustan 1984.

Ya kammala karatun lauyansa a makarantar koyon aikin lauya ta Yale, ya kuma taba aiki da rundunar sojin Amurka bayan da ya kammala karatun sakandare.

An fara zaben Vance a matsayin Sanata ne a 2022 bayan da ya doke abokin hamayyarsa na jam’iyyar Democrat Tim Ryan.

A 2016, ya kasance daya daga cikin masu sukar Trump, amma ya sauya akalar kalamansa a lokacin da ya tashi yin takararsa ta farko a 2022.

Ya yi aure a 2014, kuma yana da ‘ya’ya uku.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Next Post
Ku Tabbatar Kun Bai Wa Mabukata Shinkafar Da Aka Ba Ku – Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnoni 

Ku Tabbatar Kun Bai Wa Mabukata Shinkafar Da Aka Ba Ku - Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnoni 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.