Masharhanta sun yi maraba da matakin kasar Sin na soke haraji baki daya kan hajojin kasashen Afrika 53 da ke da huldar diplomasiyya da Sin, inda suka bayyana shi a matsayin mai muhimmanci wajen bunkasa ayyukan masana’antu a nahiyar da shigar nahiyar ana damawa da ita cikin tsarin samar da kayayyaki a duniya.
Daga ranar 1 ga watan Mayu, manufar soke haraji da ta daukaka tsarin shigar kayayyakin gona ba tare da biyan haraji ba ta fara aiki, inda ta kara tabbatar da kudurin Sin na bude kofa, kuma ana sa ran manufar za ta taimaka wajen zurfafa hadin gwiwar Sin da Afrika a harkokin cinikayya da zuba jari.
A cewar Leseko Makhetha, shugaban sashen nazarin tattalin arziki na jami’ar Lesotho, kai tsaye, manufar za ta tallafawa ayyukan masana’antu ta hanyar rage shingaye ga kayayyakin da ba a kammala sarrafawa ba da ma wadanda aka sarrafa, ba wai kawai wadanda ke bukatar sarrafawa ba.
Shi kuma Sandile Swana mai sharhi na kasar Afrika ta Kudu, ya bayyana irin manyan damarmakin da ke akwai daga samun damar shiga kasuwar kasar Sin, yana mai jinjinawa matakin a matsayin gagarumar dama ga masu fitar da kayayyaki daga Afrika.
Ya ce, manufar ta dace da burin da nahiyar ke son cimmawa zuwa shekarar 2063, da kuma kokarin hukumomin yanki kamar kungiyar raya kudancin Afrika na dunkulewa da baza komar tattalin arzikinsu.
Yana mai jaddada girman damar da Sin ta samar ga kasashen Afrika a matsayin mai muhimmanci.Shi kuwa Tabani Moyo, mai bincike a tsangayar nazarin harkokin kasuwanci da shugabanci ta jami’ar KwaZulu-Natal cewa ya yi, ya dace nahiyar Afrika ta yi amfani da damar da katafariyar kasuwar kasar Sin ta samar.
Yana cewa, dole ne kayayyakin Afrika su yi amfani da wannan dama wajen saukaka cinikayya tsakanin kasashensu da Sin, saboda girman kasuwar sayayya ta Sin da kuma masana’antun da kasar ke da su. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post