Ƙasar Turkiyya ta zama ƙasa ta biyu da ta fice daga gasar Kofin Duniya na 2026 bayan ta sha kashi da ci 1-0 a hannun Paraguay a wasan rukuni da aka buga da sanyin safiyar Asabar.
Kafin hakan, Haiti ta kasance ƙasa ta farko da aka tabbatar da ficewarta daga gasar bayan Brazil ta doke ta da ci 3-0. Haiti ta kammala wasanni biyu ba tare da samun maki ko ɗaya ba, sannan an zura mata ƙwallaye huɗu ba tare da ta ci ko guda ɗaya ba.
Ita ma Turkiyya ta kasa samun maki a wasanninta biyu na farko, bayan Scotland ta doke ta da ci 2-0 a wasan farko, sannan Paraguay ta sake doke ta da ci 1-0 a wasa na biyu, lamarin da ya tabbatar da ficewarta daga gasar.
A wani ɓangare kuma, Mexico ta zama ƙasa ta farko da ta tsallake zuwa zagaye na 32 bayan ta samu maki shida a wasanni biyu. Ƙasar ta doke Afirka ta Kudu da ci 2-0 a wasan farko, sannan ta samu nasara a kan Koriya ta Kudu a wasa na biyu.
Da wannan sakamako, Mexico ce ke jan ragamar rukunin A kuma ta tabbatar da gurbin ta a matakin gaba na gasar.















Discussion about this post