Ƙungiyar da ke fafutukar kare muhalli da yaƙi da ɗumamar yanayi da ke Jihar Kaduna (KADCCAM), ta jinjina wa hukumar samar da abinci da kuma ayyukan gona ta majalisar ɗinkin duniya, tare da kuma ma’aikatar aikin gona ta jihar, kan gudanar da bita ta kwana ɗaya a jihar.
Wannan yabo, na zuwa ne bayan samun nasarar kammala taron kwana ɗaya cikin nasara, na masu ruwa da tsaki a fannin na aikin noma.
Ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar a bangaren harkar aikin noma, Rabaran Michael Ijah Ikpa, ya bayyana haka a cikin sanarwar da ya fitar a jihar.
Manufar taron na masu ruwa da tsaki shi ne, domin samun damar tattara wa ma’aikatar bayanan da suka shafi aikin noma da kuma albarkatun ƙasa da za a a yi amfani da su daga 2026 zuwa 2030.
Ikpa ya ce, taron bitar, ya zo kan gaba, wanda kuma yake da matuƙar muhimmanci ga manoman jihar da sauran abokan haɗaka da ƙungiyoyi, waɗanda suka taimaka wajen samun cikakkun bayanai, domin ƙara habaka fannin aikin noma na jihar.
Ya ƙara da cewa, taron ya kuma taimaka, wajen yin musayar bayanai da shawarwari, musamman kan yadda za a ƙara bunƙasa noma da ƙara kula da albarkatun ƙasa a ɗaukacin faɗin jihar.
Shi ma ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyar, Kwamared Ibrahima Yakubu, ya yi nuni da cewa; tattawanar ta kasance mai inganci da aka yi a yayin taron da kuma yadda mahalarta taron suka amsa gayyata, hakan ya nuna a zahari na irin ƙarfafa haɗakar, domin cimma burin da aka sanya a gaba.
Yakubu ya jaddada cewa, fannin aikin noma, shi ne kan gaba, wajen bunƙasa fannin tattalin arziƙi da rage talauci a tsakanin al’umomomin faɗin duniya baki-ɗaya.
A cewarsa, shawarwarin da mahalarta taron suka bayar a yayin taron, za a yi amfani da su wajen samar da tsarin fannin aikin da kuma kula da albarkatun ƙasa daga 2026 zuwa 2030.
Ya kuma nanata goyon bayan ƙungiyar, wajen samar da shirye-shiryen dabarun kare ɗumamar yanayi da kula da fannin aikin noma da ƙara samar da wadataccen abinci, musamman a jihar.















Discussion about this post