• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Sakamako Aka Samu Daga Cinikin Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wadanne Sakamako Aka Samu Daga Cinikin Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan an fitar da sabbin alkaluman ciniki tsakanin Sin da kasashen waje, kuma abin lura shi ne, a farkon watanni 9 na bana, a karo na farko, kudin hajojin da kasar Sin ta fitar da su kasashen waje da ma shigo da su daga ketare ya zarce kudin Sin yuan triliyan 32, adadin da ya kai triliyan 30.8 a makamancin lokacin a bara. Ban da haka, a kowane rubu’i na wannan shekara, adadin ya zarce yuan triliyan 10, wanda kuma ya kasance na farko a makamancin lokacin a shekarun baya.

 

Alkaluman sun shaida cewa, a farkon watanni 9 na bana, kudin hajojin da kasar Sin ta fitar da su kasashen waje da ma shigo da su daga ketare ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 32.33, adadin da ya karu da kaso 5.3% kwatankwacin na bara. A yayin da ake fuskantar karin matakan kariyar ciniki da wasu kasashe suka dauka da ma kokarin farfado da tattalin arzikin duniya, yadda kasar Sin ta tabbatar da karuwar ciniki tsakaninta da kasashen ketare fiye da yadda aka yi hasashe, ba abu mai sauki ba ne.

  • Majalisar Dokokin Jigawa Ta Amince Da Ƙudirin Kafa Hukumar Wutar Lantarki
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 20 Da Kafa Cikakkiyar Dangantakar Abokantaka Bisa Manyan Tsare-tsare Tsakanin Sin Da Italiya A Milan

In mun yi la’akari da yanayin ciniki a cikin gidan kasar, hajojin da kasar Sin ta samar suna da karfin takara sakamakon yadda ake samun cikakken tsarin samar da kayayyaki da saurin ci gaban fasahohi a kasar, matakin da ya aza tushen rika fadada kasuwanninsu a duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Sai kuma in mun duba yanayin ketare, yadda bukatun kasuwannin ketare suka farfado ya samar da kyawawan sharuda ga kasar wajen fitar da kayayyakinta zuwa gare su. Rahoton da kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO ta fitar a kwanan baya ya kyautata hasashenta kan yawan cinikin hajojin na duniya cikin shekarar bana.

 

Ciniki tsakanin kasar Sin da kasashen ketare ya kuma samar wa kasa da kasa kayayyakin zamani masu inganci wadanda kuma ke kiyaye muhallin duniya. A halin yanzu, kasar Sin na fitar da motoci amsu amfani da lantarki da baturan Lithium da ma farantan samar da wuta daga hasken rana zuwa kasashe da shiyyoyi sama da 200, wadanda ba ma kawai inganta samar da kayayyaki a duniya suka yi ba, har ma da taimakawa wajen saukaka matsalar hauhawar farashi, tare da bayar da babbar gudummawa wajen tinkarar sauyin yanayin duniya.

 

A takaice dai, yadda harkokin ciniki tsakanin kasar Sin da kasashen ketare ya yi ta farfadowa, ya shaida ingancin tattalin arzikin kasar Sin, kuma shi ne dalilin da ya sa wasu hukumomin hada-hadar kudi na duniya, ciki har da Goldman Sachs, suka kyautata hasashensu kan bunkasuwar tattalin arzikinta a shekarar da muke ciki. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Li Qiang Ya Halarci Taron Majalisar Shugabannin Gwamnatocin Kasashe Mambobin SCO Karo Na 23

Next Post

Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

Related

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

3 hours ago
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

4 hours ago
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700
Daga Birnin Sin

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

5 hours ago
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

6 hours ago
Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi
Daga Birnin Sin

Hanya Mai Salon Musamman Da Kasar Sin Take Bi Wajen Raya Harkokin Kudi

7 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Hada Hannun Matasa Da Yaran Sin Da Amurka Na Shekarar 2025

17 hours ago
Next Post
Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.