• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Sakamako Aka Samu Daga Cinikin Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare

by CGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Wadanne Sakamako Aka Samu Daga Cinikin Tsakanin Sin Da Kasashen Ketare
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan an fitar da sabbin alkaluman ciniki tsakanin Sin da kasashen waje, kuma abin lura shi ne, a farkon watanni 9 na bana, a karo na farko, kudin hajojin da kasar Sin ta fitar da su kasashen waje da ma shigo da su daga ketare ya zarce kudin Sin yuan triliyan 32, adadin da ya kai triliyan 30.8 a makamancin lokacin a bara. Ban da haka, a kowane rubu’i na wannan shekara, adadin ya zarce yuan triliyan 10, wanda kuma ya kasance na farko a makamancin lokacin a shekarun baya.

 

Alkaluman sun shaida cewa, a farkon watanni 9 na bana, kudin hajojin da kasar Sin ta fitar da su kasashen waje da ma shigo da su daga ketare ya kai kudin Sin yuan tiriliyan 32.33, adadin da ya karu da kaso 5.3% kwatankwacin na bara. A yayin da ake fuskantar karin matakan kariyar ciniki da wasu kasashe suka dauka da ma kokarin farfado da tattalin arzikin duniya, yadda kasar Sin ta tabbatar da karuwar ciniki tsakaninta da kasashen ketare fiye da yadda aka yi hasashe, ba abu mai sauki ba ne.

  • Majalisar Dokokin Jigawa Ta Amince Da Ƙudirin Kafa Hukumar Wutar Lantarki
  • An Yi Bikin Murnar Cika Shekaru 20 Da Kafa Cikakkiyar Dangantakar Abokantaka Bisa Manyan Tsare-tsare Tsakanin Sin Da Italiya A Milan

In mun yi la’akari da yanayin ciniki a cikin gidan kasar, hajojin da kasar Sin ta samar suna da karfin takara sakamakon yadda ake samun cikakken tsarin samar da kayayyaki da saurin ci gaban fasahohi a kasar, matakin da ya aza tushen rika fadada kasuwanninsu a duniya.

 

Labarai Masu Nasaba

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Sai kuma in mun duba yanayin ketare, yadda bukatun kasuwannin ketare suka farfado ya samar da kyawawan sharuda ga kasar wajen fitar da kayayyakinta zuwa gare su. Rahoton da kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO ta fitar a kwanan baya ya kyautata hasashenta kan yawan cinikin hajojin na duniya cikin shekarar bana.

 

Ciniki tsakanin kasar Sin da kasashen ketare ya kuma samar wa kasa da kasa kayayyakin zamani masu inganci wadanda kuma ke kiyaye muhallin duniya. A halin yanzu, kasar Sin na fitar da motoci amsu amfani da lantarki da baturan Lithium da ma farantan samar da wuta daga hasken rana zuwa kasashe da shiyyoyi sama da 200, wadanda ba ma kawai inganta samar da kayayyaki a duniya suka yi ba, har ma da taimakawa wajen saukaka matsalar hauhawar farashi, tare da bayar da babbar gudummawa wajen tinkarar sauyin yanayin duniya.

 

A takaice dai, yadda harkokin ciniki tsakanin kasar Sin da kasashen ketare ya yi ta farfadowa, ya shaida ingancin tattalin arzikin kasar Sin, kuma shi ne dalilin da ya sa wasu hukumomin hada-hadar kudi na duniya, ciki har da Goldman Sachs, suka kyautata hasashensu kan bunkasuwar tattalin arzikinta a shekarar da muke ciki. (Lubabatu Lei)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Li Qiang Ya Halarci Taron Majalisar Shugabannin Gwamnatocin Kasashe Mambobin SCO Karo Na 23

Next Post

Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

Related

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Daga Birnin Sin

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

10 hours ago
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

11 hours ago
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori
Daga Birnin Sin

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

12 hours ago
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

14 hours ago
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

15 hours ago
UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba

1 day ago
Next Post
Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

Masu Gida Sun Yi Ruwan Kwallaye A Enugu

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.