Wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma mataimakin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin Losang Jamcan, zai halarci bikin rantsuwar kama aiki ta shugabannin kasashen Djibouti da Uganda bisa gayyatar gwamnatocin kasashen biyu.
A birnin Djibouti, Losang Jamcan zai halarci rantsuwar kama aiki ta zababben shugaban kasar Ismail Omar Guelleh, a ranar Asabar 9 ga watan nan na Mayu, kana zai isa birnin Kampala inda shugaba mai ci Yoweri Kaguta Museveni ma zai sha rantsuwar ci gaba da mulki a ranar Talata 12 ga wata, kamar dai yadda kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya bayyana hakan a yau Laraba.
Gabanin hakan, bisa gayyata daga gwamnatin Costa Rica, wakilin musamman na shugaban kasar Sin Xi Jinping, kuma shugaban hukumar bunkasa hadin gwiwar kasa da kasa Chen Xiaodong, zai halarci bikin mika mulki ga sabuwar gwamnatin kasar a birnin San Jose, tsakanin gobe Alhamis 7 zuwa jibi Juma’a 8 ga watan nan. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post