Kwanan nan ne, babban darektan hukumar UNESCO ta Majalisar Dinkin Duniya, Khaled El-Enany, ya zanta da wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG a takaice.
Da yake tsokaci kan ziyararsa ta farko a kasar Sin bayan kama aikin shugabancin UNESCO, Khaled El-Enany ya bayyana cewa, ziyarar za ta kasance wata muhimmiyar alama ta daban ta ci gaban abotar kasar Sin da UNESCO.
Khaled El-Enany ya yaba da ra’ayin shugaba Xi Jinping dangane da musanya gami da koyon wayewar kan juna, inda ya ce, “muna bukatar sauraren juna, da yin kokari tare da kara samun fahimtar juna. Wannan shi ne ra’ayin da shugaba Xi Jinping ya jaddada yayin ziyararsa a hukumar UNESCO a shekara ta 2014.”
Kazalika, Khaled El-Enany ya ce, akwai bukatar sassan kasa da kasa su koyi dabarun kasar Sin, don samun irin dimbin nasarorin da ta samu a ’yan shekarun nan a fannonin da suka shafi samar da ilimi na dijital da amfani da fasahar kirkirarriyar basira wato AI. (Murtala Zhang)















Discussion about this post