Jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana ƙwarin gwiwarsa cewa Peter Obi zai lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Kwankwaso ya yi wannan bayani ne a ranar Juma’a yayin tabbatar da ‘yan takarar da aka amince da su na jam’iyyar NDC a Jihar Kano.
Ya ce an gudanar da zaɓen cikin lumana kuma an samu haɗin kai a cikin jam’iyyar.
A cewarsa, duk da yawan masu neman takara a wasu mazaɓu, shugabanni sun cimma matsaya ta hanyar tattaunawa da fahimtar juna.
“Ni ina magana ne a kan Peter Obi. Shi ne zai daga tutar jam’iyyarmu, kuma da yardar Allah, a ranar 29 ga watan Mayu na shekara mai zuwa, zai zama Shugaban Jamhuriyar Tarayyar Nijeriya,” in ji Kwankwaso.
Ya buƙaci ‘yan jam’iyyar da su ci gaba da haɗa kai gabanin zaɓen 2027, tare da yabawa yadda aka gudanar da tsarin zaɓen fidda-gwani cikin nasara.
A wajen taron, an tabbatar da tsohon mataimakin gwamnan Kano, Abdulsalam Gwarzo, a matsayin ɗan takarar gwamna, yayin da Nasiru Yusuf Gawuna ya zama ɗan takarar Sanatan Kano ta Tsakiya.
Haka kuma an amince da sauran ‘yan takara na Majalisar Tarayya da Majalisar Jiha gabanin zaɓen.
A nasa ɓangaren, Gwarzo ya yi alƙawarin gudanar da mulki da zai haɗa kan kowa da kowa idan aka zaɓe shi a matsayin gwamna a 2027.















Discussion about this post