Ministan harkokin wajen kasar Sin, Wang Yi, ya bayyana a ranar Asabar da ta gabata cewa, ya kamata a kyautata tsarin jagorancin duniya ta hanyar yin gyare-gyare domin daidaita tsarin tarihi.
Wang, mamba a ofishin siyasa na kwamitin tsakiya na jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a zaman taron da aka yi mai lakabin “Sin a duniya” a babban taron tsaro na Munich da ke gudana.
Wang ya ce, al’amuran kasa da kasa sun kara shiga garari da kwan-gaba-kwan-baya a cikin shekarar da ta gabata. Amfani da irin tsarin rayuwar namun daji da yin gaban-kai sun kara yawaita, kuma dalilin zaman lafiya da ci gaban dan Adam sun hau kan wani sabon siradi.
Wang ya ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarar inganta jagorancin duniya, inda ya yi kira da a aiwatar da daidaiton ‘yancin mallakar kasa, da bin dokokin kasa da kasa, da tsarin mabambantan bangarori, da amfani da tsari mai fifita al’umma, da aiwatar da matakai na hakika, a kokarin da ake yi na gina tsarin jagorancin duniya mafi adalci da kuma cancanta.
Wang ya yi kira da a yi kokarin cimma tsagaita bude wuta da sake gina Gaza, yana mai cewa aiwatar da shawarar kafa kasashe biyu, da maido da yin gaskiya da adalci ga al’ummar Falasdinu, wani nauyi ne da al’ummomin kasashen duniya ba za su iya guje masa ba. Sannan, halin da ake ciki a Iran ya shafi yanayin zaman lafiya gaba daya a yankin gabas ta tsakiya, don haka ya kamata dukkan bangarorin da abin ya shafa su yi taka-tsan-tsan don kauce wa haddasa sabuwar fitina.
Kazalika, bisa yadda rikicin Ukraine ya bude kofar tattaunawa, Wang ya ce, kamata ya yi dukkan bangarorin da abin ya shafa su yi amfani da wannan damar wajen kokarin cimma daidaito, da yarjejeniya mai dorewa, da kashe wutar musabbabin tashe-tashen hankula, da samar da zaman lumana na dogon lokaci a yankin Turai. Game da batun Venezuela kuma, bai kamata a ketare bin dokokin kasa da kasa ba, kuma dole ne a kiyaye ka’idar ‘yancin mallakar kasa.
Wang ya ce, kasar Sin za ta kasance mai ba da gudummawa sosai wajen samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaban tarihi, kuma za ta sa kaimi ga gina al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai-daya ga bil’adama. (Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post