Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya zanta da takwaransa na kasar Amurka Marco Antonio Rubio ta wayar tarho a ranar Talatar da ta gabata.Yayin zantawarsu, Wang Yi ya ce a watan Mayun bana, shugaba Xi Jinping da shugaba Donald Trump, sun cimma matsayi daya kan kafa dangantaka mai karko bisa manyan tsare-tsare a tsakanin Sin da Amurka, da wasu sauran muhimman batutuwa, a yayin ziyarar shugaba Trump a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.
Sun kuma ba da jagoranci bisa manyan tsare-tsare game da yadda za a raya dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasar Amurka cikin shekaru 3 masu zuwa, ko ma cikin dogon lokaci mai zuwa. Don haka a cewarsa ya kamata bangarorin biyu su tsaya tsayin daka wajen bin wannan hanya, tare da warware matsalolin dake gabansu.
Haka kuma, ya ce ya kamata bangarorin biyu su bi ka’idar nuna adalci, da girmama juna, da kuma tallafa wa juna, domin mayar da ra’ayi daya da shugabannin biyu suka cimma, zuwa manufofi da matakai na zahiri.
Kazalika, ya kamata bangarorin biyu su kara inganta jerin hadin gwiwar dake tsakaninsu, tare da tsara karin aikace-aikace masu inganci, yayin da suke rage sabani tsakaninsu. A sa’i daya kuma, su yi kandagarkin tarin kalubaloli.
Ya ce batun yankin Taiwan wani muhimmin batu ne da ya shafi dukkanin fannoni, ya kamata kasar Amurka ta mayar da matukar hankali kan harkokin dake shafar yankin Taiwan na kasar Sin.
A daya bangaren kuma, bangarorin biyu sun cimma matsayi daya cewa, zantawar ministocin harkokin wajen kasashen biyu a wannan karo, ta yi matukar ma’ana. Sun kuma amince da aiwatar da ra’ayoyin bai daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma yadda ya kamata, tare da ci gaba da yin mu’amala ta mabambanta hanyoyi idan akwai bukata. (Mai Fassara: Maryam Yang)














