Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Taiwan yanki ne na kasar Sin da ba za a iya balle shi ba, kuma batun Taiwan lamari ne na cikin gidan kasar Sin, kana warware batun Taiwan ya shafi kasar Sin ne ita kadai.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan a jiya Jumma’a, yayin taron manema labarai na yau da kullum, lokacin da yake amsa tambaya dangane da tsokacin firaministar Japan da shugaban Amurka, game da muhimmancin wanzar da zaman lafiya da daidaito a zirin Taiwan, ya ce yayin da ake fatan cimma wannan buri, dole ne a bayyana matukar adawa da manufar ’yan a ware ta yunkurin neman ’yancin kan Taiwan. (Saminu Alhassan)
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
ADVERTISEMENT















Discussion about this post