Yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping, wanda kuma shi ne babban sakataren kwamitin koli na jam’iyyar kaminis ta kasar, ya aike da sako ga To Lam, don taya shi murnar lashe zaben shugaban kasar Vietnam.
A cikin sakonsa, Xi Jinping ya bayyana cewa, yana mayar da hankali sosai kan ci gaban dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma jam’iyyar kwaminis ta Sin da ta Vietnam, ya kuma bayyana fatansa na yin aiki tare da babban sakatare, kuma shugaban kasa To Lam, a kokarin raya kasashensu, tare kuma da samar da tabbas da kyakkyawan karfi ga shiyyarsu har ma da duniya baki daya.
A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang ya aike da sako ga Le Minh Hung, don taya shi murnar lashe zaben firaministan kasar Vietnam. (Bilkisu Xin)















Discussion about this post