ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Zai Jagoranci Taron Kolin Sin Da Asiya Ta Tsakiya

by CMG Hausa
3 years ago
Asiya

Ma’aikatar harkokin wajen Sin ta sanar da cewa, za a gudanar da taron kolin Sin da Asiya ta Tsakiya daga ranar 18 zuwa 19 ga watan Mayu a birnin Xi’an dake lardin Shaanxi, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai jagoranci taron.

Kakakin ma’aikatar Hua Chunying, ta sanar da ewa, shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev, da shugaban kasar Kyrgyzstan Sadyr Nurgozhoevich Japarov, da shugaban Tajikistan Emomali Rahmon, da shugaban Turkmenistan Serdar Berdimuhamedov da kuma shugaban Uzbekistan Shavkat Miromonovich Mirziyoyev, za su hallarci taron bisa gayyatarsu da aka yi musu.

  • Xi Jinping Ya Jagoranci Zama Na Farko Na Kwamitin Koli Kan Harkokin Kudi Da Tattalin Arziki Karo Na 20

Har ila yau, bisa gayyatar da Shugaba Xi ya yi musu, Shugabannin Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev, da shugaban Kyrgyzstan Sadyr Nurgozhoevich Japarov, da shugaban Tajikistan Emomali Rahmon da shugaban Uzbekistan Shavkat Miromonovich Mirziyoyev za su yi ziyarar aiki a kasar Sin daga ranar 16 zuwa 20 ga watan Mayu.

ADVERTISEMENT

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, taron kolin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya, muhimmin taro ne na farko da kasar Sin za ta gudanar a bana, kana shi ne karo na farko da shugabannin kasar Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya da abin ya shafa, za su halarci taron koli kai tsaye a cikin shekaru 31 bayan kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu, don haka taron kolin yana da babbar ma’ana a tarihin raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana a yau cewa, za a gudanar da taron kolin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya tun daga ranar 18 zuwa 19 ga watan Mayu a birnin Xi’an dake lardin Shaanxi.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Wang Wenbin ya yi bayani da cewa, a yayin taron kolin, shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gabatar da muhimmin jawabi, sannan shugabannin kasa da kasa masu halartar taron, za su waiwayi tarihin raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya, da musayar ra’ayoyi kan manyan batutuwan kasa da kasa da yankuna ciki har da tsarin raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya da hadin gwiwarsu da sauransu, kana za su daddale wata muhimmiyar takardar siyasa tare.

Kakakin ya yi imanin cewa, bisa kokarin da bangarori daban daban suka yi, za a tsara taswirar raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Asiya ta Tsakiya, da kuma bude sabon babi na hadin gwiwarsu baki daya. (Safiyah Ma, Zainab Zhang)

Asiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Xi Ya Gana Da Wakilan Taron Sinawa Mazauna Ketare Karo Na 10

Xi Ya Gana Da Wakilan Taron Sinawa Mazauna Ketare Karo Na 10

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.