Mutane bakwai sun rasa rayukansu yayin da wasu shida suka jikkata sakamakon wani rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyukan Lanzai da Dosho da ke ƙaramar hukumar Darazo a jihar Bauchi. Har ila yau, rikicin ya haddasa asarar dukiyoyi da dama, ciki har da ƙone gidaje da rugar dabbobi.
Kakakin rundunar ‘yansandan jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya ce lamarin ya fara ne bayan wasu da ake zargin makiyaya ne sun kai hari kan manoma da ke aikin zuba taki a gonakinsu da ke wajen ƙauyen Lanzai. Daga bisani wasu matasa daga ƙauyen suka kai harin ramuwar gayya zuwa Dosho, inda suka banka wa sassan ƙauyen wuta.
A cewarsa, kimanin ruga 50 ne suka ƙone ƙurmus tare da lalacewar dukiyoyi masu yawa. Ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun gaggauta isa yankin domin daƙile rikicin, da dawo da zaman lafiya da kuma fara bincike kan musabbabin tashin hankalin.
Kwamishinan ‘yansandan jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike tare da tabbatar da hukunta duk wanda aka samu da hannu a rikicin. Ya kuma yi kira ga mazauna yankunan da su kwantar da hankalinsu tare da kauce wa ɗaukar doka a hannunsu.















Discussion about this post