Rundunar ‘yansandan jihar Sakkwato ta daƙile wani harin ‘yan bindiga a ƙauyen Imasa Matankari da ke ƙaramar hukumar Tureta, inda ta kwato shanu 25 da maharan suka sace yayin harin.
Kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufai, ya ce lamarin ya faru ne ranar 2 ga Yuni, 2026 lokacin da gungun ‘yan bindigar suka kai hari ƙauyen da ke kusa da iyakar jihohin Sakkwato da Zamfara, inda suka yi harbe-harbe tare da sace shanun wasu mazauna yankin.
Ya ce bayan samun rahoton harin, jami’an VCRU da na Anti-Kidnapping tare da haɗin gwuiwar sojojin FOB suka bazama yankin, inda suka tare hanyoyin da maharan za su iya bi wajen tserewa sannan suka fafata da su.
A sakamakon musayar wutar, maharan sun tsere zuwa dajin Kuruwa tare da barin dukkan shanun da suka sace. Rundunar ta ce an mayar da shanun ga masu su, yayin da ake ci gaba da farautar wadanda suka tsere tare da kara tsaurara matakan tsaro a yankin.















Discussion about this post