Mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da wasu shida suka jikkata a wani rikici tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyukan Lanzai da Dosho da ke ƙaramar hukumar Darazo a Jihar Bauchi.
Rikicin ya faru ne a ranar Alhamis, inda kuma ya jawo asarar dukiya, ciki har da gidaje da kayan amfanin jama’a da suka kai darajar dubban Naira.
Yadda Rikicin Ya Samo Asali
Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya fara ne lokacin da wasu da ake zargin makiyaya suka kai wa manoma da ke aiki a gonakinsu hari a wajen ƙauyen Lanzai.
Bayan haka, wasu matasa daga Lanzai sun mayar da martani ta hanyar kai farmaki zuwa ƙauyen Dosho, inda makiyaya ke zaune.
A wajen, an banka wa wasu gidaje wuta, inda aka ce kusan ruga 50 sun ƙone gaba ɗaya tare da lalata dukiyoyi da dama.
Martanin ‘Yansanda
Kakakin ‘yansandan Jihar Bauchi, SP Nafiu Habib, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin tabbatar da zaman lafiya a yankunan da abin ya shafa.
Ya ce rikicin ya yi sanadin mutuwar mutane bakwai, yayin da shida suka jikkata kuma suke karɓar magani a asibiti.
Bayan samun rahoton, an tura jami’an tsaro na musamman zuwa yankin domin daƙile rikicin da kuma fara bincike kan abin da ya faru.
Bincike Da Kira A Zauna Lafiya
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Bauchi, CP Sani-Omolori Aliyu, ya bayar da umarnin gudanar da bincike domin gano musabbabin rikicin.
Ya kuma yi gargaɗi cewa duk wanda aka samu da hannu a rikicin ko ɗaukar doka a hannunsa zai fuskanci hukunci.
Hukumomi sun kuma yi kira ga shugabannin al’umma da mazauna yankin da su kwantar da hankali tare da guje wa ɗaukar doka a hannu domin kauce wa ƙarin rikici.














Discussion about this post