Gabanin bikin ranar yara ta kasa da kasa, babban sakataren kwamitin kolin JKS, kuma shugaban kasar, kana shugaban kwamitin koli na rundunar soja Xi Jinping, ya aike da amsar wasika ga yara masu jagorantar cibiyar tunawa da babban taron kasa karo na farko na JKS, da cibiyar tunawa da juyin juya halin Nanhu, inda a cikin wasikar ya karfafa musu gwiwa, tare da taya su, da ma dukkan yaran kasar Sin murnar bikin ranar yara.
A cikin wasikarsa, Xi ya ce, “Ina matukar farin ciki da na fahimci cewa kun samu karuwa ta hanyar sanin bayanan tarihi, da labaran juyin juya hali, da ma labaran jaruman JKS, a tsohon wurin kaddamar da babban taron kasa karo na farko na JKS, da kuma gefen tafkin Nanhu.” Tun daga shekarar 2021, ake shiryawa yara mambobin kungiyar yaran kasar Sin daga sassan kasar daban daban, damar ziyartar wuraren tunawa da tarihin JKS, don su koyi tarihin jam’iyyar da kuma gabatar musu da labaranta. (Safiyah Ma)















Discussion about this post