ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yaƙin Gabas Ta Tsakiya: Masu Tafiya Umrah Daga Nijeriya Na Fuskantar Cikas

by Sani Anwar
4 months ago
Umrah

Akwai wani yanayi na rashin tabbas a tsakanin kamfanoni masu zaman kansu da kuma matafiya Umara daga Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya, yayin da yaƙin Iran da Amurka ke ci gaba da yin illa ga ayyukan jiragen sama da sauran harkokin kasuwanci.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, ɗimbin al’ummar musulmi suna zuwa ƙasar Saudiyya a cikin watan Ramadan, domin aikin Umara, inda sama da masu ibada miliyan 122 suka ziyarci ƙasar a cikin watan Ramadana na shekarar 2025.

  • WSCIJ Ta Naɗa Farfesa Umaru Pate A Kwamitin Amintattu
  • Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Sai dai kuma, tashin hankalin da ake fama da shi a Gabas ta Tsakiya, tare da rufe muhimman hanyoyin jiragen sama, irin su Doha da Dubai, na tilastawa maniyyata daga Nijeriya sake duba shirin tafiyar.

ADVERTISEMENT

Tashe-tashen hankula sun ƙara zama abubuwan lura a kan tsaro da amincin jirgin da kuma zuwa a kan lokaci, domin gudanar da ibada, lamarin da ya sa mutane da dama, ba su da tabbas a kan ko za su samu damar zuwa aikin nasu na Umara a bana.

Ƙasashen Iran da Iraƙi da Isra’ila da Syria da Kuwait da Ƙatar da kuma Hadaddiyar Daular Larabawa, sun sanar da cewa; an rufe sararin samaniyarsu, bayan da Amurka da Isra’ila suka kai wa Iran hari, lamarin da ya kawo dakatar da zirga-zirgar jiragen sama na farar hula a Gabas ta Tsakiya.

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Fitattun kamfanonin jiragen sama da suka dakatar ayyukan, sun haɗa da kamfanin Emirates, Etihad, Ƙatar Airways, Air France, British Airways, Syria Air, Air India, Turkish Airlines, EgyptAir, Lufthansa da kuma Habasha Airlines.

Sai dai, sauran kamfanonin jiragen saman irin su Saudi Arabian Airlines, na ci gaba da zirga-zirgar jiragen sama zuwa ƙasar, saboda Saudiyya ba ta rufe sararin samaniyarta a hukumance ba, duk da katsewar yankin.

Sararin samaniyar Saudiyya na ci gaba da karɓar jiragen farar hula, bayan hare-haren ramuwar gayya a yankin Gabas ta Tsakiya.

Duk da cewa dai kuma, hare-haren makami mai linzami da jiragen sama na baya-bayan nan da aka kai kan ababen more rayuwa na yankin Gulf, ciki har da harin da aka kai a wata cibiyar matatar mai a Saudiyya, ya haifar da fargabar cewa; Riyadh na iya sanya takunkumin sararin samaniya, idan rikicin ya ƙara tsananta.

Mahajjata suna bayyana ra’ayoyinsu kusan iri ɗaya, waɗanda suka zanta da Daily trust, sun bayyana ra’ayoyinsu daban-daban, inda wasu ke tunanin soke tafiye-tafiyen nasu.

Alhaji Auwal Sani, wanda ya yi niyyar zuwa aikin Umara a Kano, ya ce; an dakatar da tafiyasa wadda ya shirya yi a ranar Litinin.

“Zan yi tafi ne a jirgin Ƙatar Airways, amma sai na samu saƙo daga wurinsu cewa; an buɗe tikitin bayan an soke shi, haka kuma ba a ba ni bizar ba har yanzu, kuma na shirya tafiya tare da iyalina a yau, amma ga mu duk a maƙale, Allah ne mafi sanin abin da ya fi dacewa da mu.

“Sun ce za a buɗe sararin samaniya a ranar 6 ga watan Maris, sannan kuma za a ba mu biza, domin mu tafi,” in ji shi.

Salihu Shu’aibu, wanda ke shirin tafiya Umrah, ya ce; halin da ake ciki a halin yanzu ya sa shi cikin damuwa ƙwarai da gaske.

“Gaskiya, abin da yake faruwa, yana ba ni tsoro shi yasa nake tunanin ko kawai ma na soke tafiyar tawa kwata-kwata,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa, tsoron abin da ba a sani ba, ya dabaibaye maniyyata da dama a Jihar Kwara.

Umrah
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa
Manyan Labarai

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta
Manyan Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Next Post
Kamfanin Sin Ya Bude Babban Titin Nairobi Kyauta Ga Masu Ababen Hawa Da Suka Makale Saboda Ambaliya

Kamfanin Sin Ya Bude Babban Titin Nairobi Kyauta Ga Masu Ababen Hawa Da Suka Makale Saboda Ambaliya

LABARAI MASU NASABA

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.