Yau Asabar 15 ga watan nan ne ake cika shekaru 81 da mika wuyar da kasar Japan ta yi ba tare da gindaya wani sharadi ba a yayin yakin duniya na biyu. A ranar kuma, firaministar Japan, Sanae Takaichi ta bayar da kudin hadaya ga haikalin Yasukuni, inda aka ajiye alluna masu dauke da sunayen manyan kusoshin kasar guda 14 da suka aikata munanan laifukan yaki yayin yakin duniya na biyu, haka kuma akwai wasu jami’an gwamnati gami da ’yan jam’iyyar LDP da suka ziyarci wurin.
A wannan muhimmiyar rana, wasu ’yan siyasar Japan masu ra’ayin rikau sun sake ziyartar haikalin Yasukuni, al’amarin da ya kasance rashin girmama adalcin tarihi, da kalubalantar wayewar kan dan Adam, kana, tsokana ga odar sassan kasa da kasa da aka shimfida bayan yakin duniya na biyu.
A ranar 15 ga watan Agusta na shekara ta 1995, firaministan kasar Japan na lokacin, Murayama Tomiichi ya gabatar da jawabin amincewa da kura-kuran da kasarsa ta aikata a bangaren aiwatar da manufofin kasa, har ma suka kai ta ga hawa tafarkin kaddamar da yaki, inda kuma ya ce ya kamata Japan ta yi da-na-sanin abun da ta yi a tarihi, da kuma koyon darussa.
Amma a halin yanzu, shugabannin Japan na yin wani yunkuri na sake jefa kasar cikin mummunan hali.
Game da aika-aikar Japan ta tallata sabon ra’ayin nuna fin karfin soja, ya kamata sassan kasa da kasa su dauki matakan hanawa, da kiyaye zaman odar kasa da kasa da aka shimfada bayan yakin duniya na biyu, domin bai kamata a bari abun bakin-cikin na tarihi ya sake faruwa ba. (Murtala Zhang)














