ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

by Bello Hamza
3 months ago
Dantsoho

Tun bayan naɗa shi a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa a shekarar 2024, kaɗan ne suka yi hasashen irin gagarumin sauyin da zai kawo. Ba ɗan siyasa ne da aka kawo daga waje ba, sai dai ƙwararren masani ne a fannin sufurin teku wanda ya fara aiki da NPA tun a shekarar 1994 a matsayin ɗan yi wa ƙasa hidima (NYSC), inda ya ci gaba da hawa matakai a hankali tare da jajircewa halin da ya zama ginshiƙin shugabancinsa.

Kafin naɗin nasa, Dantsoho ya gaji wani tsari mai rikitarwa. Manyan tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya, wato Apapa da Tin Can Island, an gina su tun shekaru da dama da suka wuce. Apapa ta cika shekara 100 a 2022, yayin da Tin Can ke kusan shekara 50 da kafuwa. Waɗannan tashoshi na kogin ruwa ne, ba su da zurfi sosai don karɓar manyan jiragen ruwa na zamani da ke mamaye harkokin kasuwancin duniya a yau. Haka kuma, wuraren sauke kaya (berths) sun tsufa, yayin da yawan kaya ya yi musu yawa.

  • Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz
  • Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano
  • ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa
  • Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin
  • Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Salon aikinsa ya kasance mai tsari da nazari, wanda ya samo asali daga ƙwarewar da ya tara tsawon shekaru da kuma ci gaba da koyo. Ya fahimci cewa Nijeriya, mai yawan jama’a sama da miliyan 230 kuma mafi girman tattalin arziki a Afirka, na buƙatar tsarin tashoshin jiragen ruwa da ya dace da burinta na ƙasa.

ADVERTISEMENT

Shirin da ya tsara ya haɗa da sabunta tsofaffin kayayyakin more rayuwa, gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi, da kuma amfani da sabbin fasahohin zamani na dijital. Ƙaddamar da aikin tashar jiragen ruwa ta Lekki Deep Seaport a Legas ya zama muhimmin ginshiƙi na wannan hangen nesa, wanda ke nuna sabon farfaɗowar harkar sufurin teku a Nijeriya.

Hangen nesan Dantsoho bai tsaya a Legas kaɗai ba. A yankin Neja Delta, inda tashoshin jiragen ruwa na Warri, Koko, Sapele da Burutu suka lalace tsawon shekaru, ya ƙaddamar da wani babban shiri na farfaɗo da su domin dawo da ƙarfinsu na aiki, inganta kayayyakin more rayuwa da kuma haɓaka tattalin arziki a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

Jagorancinsa ya samu karɓuwa a matakin ƙasa da ƙasa. A watan Agustan 2025, an zaɓe shi a matsayin Mataimakin Shugaban nahiyar Afirka na International Association of Ports and Harbors, wanda ya sa ya shiga sahun gaba wajen tsara manufofin tashoshin jiragen ruwa a duniya.

Haka kuma, watanni kaɗan kafin hakan, ya zama ɗan Nijeriya na farko da ya shugabanci Ƙungiyar Gudanar da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Yammaci da Tsakiyar Afirka, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayinsa a matsayin ƙwararre a fannin sufurin teku a yankin.

Duk da waɗannan lambobin yabo, ya ci gaba da mayar da hankali kan ci gaban cikin gida, inda ya samu jarin Dala biliyan 1.1 domin gyara tsofaffin tashoshin jiragen ruwa, tare da ƙulla haɗin gwiwa domin gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi a Badagry, Akwa Ibom da Calabar.

A ƙarƙashin jagorancinsa, Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa ba kawai ta samar da ayyuka ba ne, har ma ta ɗaga matsayin inganci, sauri da ƙwarewa. Yayin da jiragen ruwa ke ƙara girma, aka zurfafa hanyoyin ruwa, kuma aka inganta tsarin aiki ta hanyar fasaha, tasirin Dantsoho ya fito fili wani fanni na sufurin teku da aka sake gina shi ba da hayaniya ba, sai dai da ƙoƙari mai ɗorewa da jajircewar mutum guda da ya sadaukar da rayuwarsa wajen kai tashoshin jiragen ruwan Nijeriya zuwa makoma mai albarka.

MASU ALAKA

NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN
Tattalin Arziki

Rage Farashin Mai Na Ɗangote: Dillalan Man Fetur Sun Yi Burus Da Sauya Nasu Farashin

June 27, 2026
Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani
Tattalin Arziki

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
Tattalin Arziki

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Next Post
An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Montenegro Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 7, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.