ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

by Bello Hamza
2 months ago
Dantsoho

Tun bayan naɗa shi a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa a shekarar 2024, kaɗan ne suka yi hasashen irin gagarumin sauyin da zai kawo. Ba ɗan siyasa ne da aka kawo daga waje ba, sai dai ƙwararren masani ne a fannin sufurin teku wanda ya fara aiki da NPA tun a shekarar 1994 a matsayin ɗan yi wa ƙasa hidima (NYSC), inda ya ci gaba da hawa matakai a hankali tare da jajircewa halin da ya zama ginshiƙin shugabancinsa.

Kafin naɗin nasa, Dantsoho ya gaji wani tsari mai rikitarwa. Manyan tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya, wato Apapa da Tin Can Island, an gina su tun shekaru da dama da suka wuce. Apapa ta cika shekara 100 a 2022, yayin da Tin Can ke kusan shekara 50 da kafuwa. Waɗannan tashoshi na kogin ruwa ne, ba su da zurfi sosai don karɓar manyan jiragen ruwa na zamani da ke mamaye harkokin kasuwancin duniya a yau. Haka kuma, wuraren sauke kaya (berths) sun tsufa, yayin da yawan kaya ya yi musu yawa.

  • Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Salon aikinsa ya kasance mai tsari da nazari, wanda ya samo asali daga ƙwarewar da ya tara tsawon shekaru da kuma ci gaba da koyo. Ya fahimci cewa Nijeriya, mai yawan jama’a sama da miliyan 230 kuma mafi girman tattalin arziki a Afirka, na buƙatar tsarin tashoshin jiragen ruwa da ya dace da burinta na ƙasa.

ADVERTISEMENT

Shirin da ya tsara ya haɗa da sabunta tsofaffin kayayyakin more rayuwa, gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi, da kuma amfani da sabbin fasahohin zamani na dijital. Ƙaddamar da aikin tashar jiragen ruwa ta Lekki Deep Seaport a Legas ya zama muhimmin ginshiƙi na wannan hangen nesa, wanda ke nuna sabon farfaɗowar harkar sufurin teku a Nijeriya.

Hangen nesan Dantsoho bai tsaya a Legas kaɗai ba. A yankin Neja Delta, inda tashoshin jiragen ruwa na Warri, Koko, Sapele da Burutu suka lalace tsawon shekaru, ya ƙaddamar da wani babban shiri na farfaɗo da su domin dawo da ƙarfinsu na aiki, inganta kayayyakin more rayuwa da kuma haɓaka tattalin arziki a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

Jagorancinsa ya samu karɓuwa a matakin ƙasa da ƙasa. A watan Agustan 2025, an zaɓe shi a matsayin Mataimakin Shugaban nahiyar Afirka na International Association of Ports and Harbors, wanda ya sa ya shiga sahun gaba wajen tsara manufofin tashoshin jiragen ruwa a duniya.

Haka kuma, watanni kaɗan kafin hakan, ya zama ɗan Nijeriya na farko da ya shugabanci Ƙungiyar Gudanar da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Yammaci da Tsakiyar Afirka, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayinsa a matsayin ƙwararre a fannin sufurin teku a yankin.

Duk da waɗannan lambobin yabo, ya ci gaba da mayar da hankali kan ci gaban cikin gida, inda ya samu jarin Dala biliyan 1.1 domin gyara tsofaffin tashoshin jiragen ruwa, tare da ƙulla haɗin gwiwa domin gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi a Badagry, Akwa Ibom da Calabar.

A ƙarƙashin jagorancinsa, Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa ba kawai ta samar da ayyuka ba ne, har ma ta ɗaga matsayin inganci, sauri da ƙwarewa. Yayin da jiragen ruwa ke ƙara girma, aka zurfafa hanyoyin ruwa, kuma aka inganta tsarin aiki ta hanyar fasaha, tasirin Dantsoho ya fito fili wani fanni na sufurin teku da aka sake gina shi ba da hayaniya ba, sai dai da ƙoƙari mai ɗorewa da jajircewar mutum guda da ya sadaukar da rayuwarsa wajen kai tashoshin jiragen ruwan Nijeriya zuwa makoma mai albarka.

MASU ALAKA

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
Tattalin Arziki

Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe

May 29, 2026
Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
Tattalin Arziki

Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho

May 29, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tattalin Arziki

Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas

May 24, 2026
Next Post
An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.