ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

by Bello Hamza
2 months ago
Dantsoho

Tun bayan naɗa shi a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa a shekarar 2024, kaɗan ne suka yi hasashen irin gagarumin sauyin da zai kawo. Ba ɗan siyasa ne da aka kawo daga waje ba, sai dai ƙwararren masani ne a fannin sufurin teku wanda ya fara aiki da NPA tun a shekarar 1994 a matsayin ɗan yi wa ƙasa hidima (NYSC), inda ya ci gaba da hawa matakai a hankali tare da jajircewa halin da ya zama ginshiƙin shugabancinsa.

Kafin naɗin nasa, Dantsoho ya gaji wani tsari mai rikitarwa. Manyan tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya, wato Apapa da Tin Can Island, an gina su tun shekaru da dama da suka wuce. Apapa ta cika shekara 100 a 2022, yayin da Tin Can ke kusan shekara 50 da kafuwa. Waɗannan tashoshi na kogin ruwa ne, ba su da zurfi sosai don karɓar manyan jiragen ruwa na zamani da ke mamaye harkokin kasuwancin duniya a yau. Haka kuma, wuraren sauke kaya (berths) sun tsufa, yayin da yawan kaya ya yi musu yawa.

  • NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
  • Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
  • Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
  • Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Salon aikinsa ya kasance mai tsari da nazari, wanda ya samo asali daga ƙwarewar da ya tara tsawon shekaru da kuma ci gaba da koyo. Ya fahimci cewa Nijeriya, mai yawan jama’a sama da miliyan 230 kuma mafi girman tattalin arziki a Afirka, na buƙatar tsarin tashoshin jiragen ruwa da ya dace da burinta na ƙasa.

ADVERTISEMENT

Shirin da ya tsara ya haɗa da sabunta tsofaffin kayayyakin more rayuwa, gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi, da kuma amfani da sabbin fasahohin zamani na dijital. Ƙaddamar da aikin tashar jiragen ruwa ta Lekki Deep Seaport a Legas ya zama muhimmin ginshiƙi na wannan hangen nesa, wanda ke nuna sabon farfaɗowar harkar sufurin teku a Nijeriya.

Hangen nesan Dantsoho bai tsaya a Legas kaɗai ba. A yankin Neja Delta, inda tashoshin jiragen ruwa na Warri, Koko, Sapele da Burutu suka lalace tsawon shekaru, ya ƙaddamar da wani babban shiri na farfaɗo da su domin dawo da ƙarfinsu na aiki, inganta kayayyakin more rayuwa da kuma haɓaka tattalin arziki a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

Jagorancinsa ya samu karɓuwa a matakin ƙasa da ƙasa. A watan Agustan 2025, an zaɓe shi a matsayin Mataimakin Shugaban nahiyar Afirka na International Association of Ports and Harbors, wanda ya sa ya shiga sahun gaba wajen tsara manufofin tashoshin jiragen ruwa a duniya.

Haka kuma, watanni kaɗan kafin hakan, ya zama ɗan Nijeriya na farko da ya shugabanci Ƙungiyar Gudanar da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Yammaci da Tsakiyar Afirka, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayinsa a matsayin ƙwararre a fannin sufurin teku a yankin.

Duk da waɗannan lambobin yabo, ya ci gaba da mayar da hankali kan ci gaban cikin gida, inda ya samu jarin Dala biliyan 1.1 domin gyara tsofaffin tashoshin jiragen ruwa, tare da ƙulla haɗin gwiwa domin gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi a Badagry, Akwa Ibom da Calabar.

A ƙarƙashin jagorancinsa, Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa ba kawai ta samar da ayyuka ba ne, har ma ta ɗaga matsayin inganci, sauri da ƙwarewa. Yayin da jiragen ruwa ke ƙara girma, aka zurfafa hanyoyin ruwa, kuma aka inganta tsarin aiki ta hanyar fasaha, tasirin Dantsoho ya fito fili wani fanni na sufurin teku da aka sake gina shi ba da hayaniya ba, sai dai da ƙoƙari mai ɗorewa da jajircewar mutum guda da ya sadaukar da rayuwarsa wajen kai tashoshin jiragen ruwan Nijeriya zuwa makoma mai albarka.

MASU ALAKA

Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu
Tattalin Arziki

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024
Tattalin Arziki

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN
Tattalin Arziki

Kwamitin Majalisa Ya Kwato Naira Miliyan 521.76 Na VAT Daga CBN

June 8, 2026
Next Post
An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.