ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Abubakar Dantsoho Ke Bunƙasa NPA A Tsanake

by Bello Hamza
3 months ago
Dantsoho

Tun bayan naɗa shi a matsayin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa a shekarar 2024, kaɗan ne suka yi hasashen irin gagarumin sauyin da zai kawo. Ba ɗan siyasa ne da aka kawo daga waje ba, sai dai ƙwararren masani ne a fannin sufurin teku wanda ya fara aiki da NPA tun a shekarar 1994 a matsayin ɗan yi wa ƙasa hidima (NYSC), inda ya ci gaba da hawa matakai a hankali tare da jajircewa halin da ya zama ginshiƙin shugabancinsa.

Kafin naɗin nasa, Dantsoho ya gaji wani tsari mai rikitarwa. Manyan tashoshin jiragen ruwa na Nijeriya, wato Apapa da Tin Can Island, an gina su tun shekaru da dama da suka wuce. Apapa ta cika shekara 100 a 2022, yayin da Tin Can ke kusan shekara 50 da kafuwa. Waɗannan tashoshi na kogin ruwa ne, ba su da zurfi sosai don karɓar manyan jiragen ruwa na zamani da ke mamaye harkokin kasuwancin duniya a yau. Haka kuma, wuraren sauke kaya (berths) sun tsufa, yayin da yawan kaya ya yi musu yawa.

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 
  • Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka
  • Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC
  • ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Salon aikinsa ya kasance mai tsari da nazari, wanda ya samo asali daga ƙwarewar da ya tara tsawon shekaru da kuma ci gaba da koyo. Ya fahimci cewa Nijeriya, mai yawan jama’a sama da miliyan 230 kuma mafi girman tattalin arziki a Afirka, na buƙatar tsarin tashoshin jiragen ruwa da ya dace da burinta na ƙasa.

ADVERTISEMENT

Shirin da ya tsara ya haɗa da sabunta tsofaffin kayayyakin more rayuwa, gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi, da kuma amfani da sabbin fasahohin zamani na dijital. Ƙaddamar da aikin tashar jiragen ruwa ta Lekki Deep Seaport a Legas ya zama muhimmin ginshiƙi na wannan hangen nesa, wanda ke nuna sabon farfaɗowar harkar sufurin teku a Nijeriya.

Hangen nesan Dantsoho bai tsaya a Legas kaɗai ba. A yankin Neja Delta, inda tashoshin jiragen ruwa na Warri, Koko, Sapele da Burutu suka lalace tsawon shekaru, ya ƙaddamar da wani babban shiri na farfaɗo da su domin dawo da ƙarfinsu na aiki, inganta kayayyakin more rayuwa da kuma haɓaka tattalin arziki a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

Jagorancinsa ya samu karɓuwa a matakin ƙasa da ƙasa. A watan Agustan 2025, an zaɓe shi a matsayin Mataimakin Shugaban nahiyar Afirka na International Association of Ports and Harbors, wanda ya sa ya shiga sahun gaba wajen tsara manufofin tashoshin jiragen ruwa a duniya.

Haka kuma, watanni kaɗan kafin hakan, ya zama ɗan Nijeriya na farko da ya shugabanci Ƙungiyar Gudanar da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Yammaci da Tsakiyar Afirka, lamarin da ya ƙara tabbatar da matsayinsa a matsayin ƙwararre a fannin sufurin teku a yankin.

Duk da waɗannan lambobin yabo, ya ci gaba da mayar da hankali kan ci gaban cikin gida, inda ya samu jarin Dala biliyan 1.1 domin gyara tsofaffin tashoshin jiragen ruwa, tare da ƙulla haɗin gwiwa domin gina sabbin tashoshin ruwa masu zurfi a Badagry, Akwa Ibom da Calabar.

A ƙarƙashin jagorancinsa, Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta Ƙasa ba kawai ta samar da ayyuka ba ne, har ma ta ɗaga matsayin inganci, sauri da ƙwarewa. Yayin da jiragen ruwa ke ƙara girma, aka zurfafa hanyoyin ruwa, kuma aka inganta tsarin aiki ta hanyar fasaha, tasirin Dantsoho ya fito fili wani fanni na sufurin teku da aka sake gina shi ba da hayaniya ba, sai dai da ƙoƙari mai ɗorewa da jajircewar mutum guda da ya sadaukar da rayuwarsa wajen kai tashoshin jiragen ruwan Nijeriya zuwa makoma mai albarka.

MASU ALAKA

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa
Tattalin Arziki

Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa

July 25, 2026
Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC
Tattalin Arziki

Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

July 24, 2026
NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa
Tattalin Arziki

NPA Ta Goyi Bayan Yarjejeniyar Shirin Bayar Da Horo Na Musamman Domin Tafiyar Da Tashoshin Jiragen Ruwa

July 24, 2026
Next Post
An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

An Yi Bikin Ranar Sinanci Ta MDD Da Bikin Sinanci Na Bidiyo Na CMG A Geneva

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 30, Sun Ƙone Gidaje Da Shaguna A Kaduna 

July 27, 2026
Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

Kwalejin Kimiyya Ta Kogi Ta Dakatar Da Malamai Kan Zargin Lalata Da Ɗalibai Da Sauran Laifuka

July 27, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Kuri’u Za Su Yi Tasiri A Zaɓen 2027, In Ji INEC

July 27, 2026
Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Dantsoho

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Dantsoho

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.